• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Majalisar Dokokin Gombe Ba Ta Tantance Kwamishinoni Ba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Majalisar Dokokin jihar Gombe har yanzu ba ta tantance zababbun kwamishinoni 17 da gwamnan jihar Muhammadu Inuwa Yahaya ya tura mata ba, kwanaki 38 da suka wuce. 

 

A ranar 28 ga watan Yulin 2023 ne gwamna Inuwa Yahaya ya gabatar da jerin sunayen Kwamishinonin ga Majalisar Dokokin jihar, kwanaki 60 bayan rantsar da shi a matsayin gwamna karo na biyu kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanadar.

  • Rage Radadi: Gwamnatin Gombe Ta Amince Da Karin Albashin N10, 000 Ga Kowani Ma’aikaci

Sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, shi ne ya mika jerin sunayen ga akawun Majalisar Dokokin jihar, Barista Rukaiyatu A. Jalo, daga baya kakakin Majalisar, Abubakar Mohammed Luggerewo ya gabatar da sunayen a gaban kwaryar Majalisar.

Shida daga cikin zababbun Kwamishinonin sun yi aiki da Inuwa a zangonsa na farko su ne Dakta Habu Dahiru (Yamaltu/Deba), Barista Zubairu Mohammed Umar (Funakaye), Dr Aishatu Umar Maigari, Muhammad Gambo Magaji (Dukku), Alhaji Nasiru Mohammed Aliyu (Yamaltu/Deba) da Sanusi Ahmed Maidala (Akko), su na cikin zababbun mambobin majalisar zartaswa ta jihar 17.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

 

11 da suka kasance sabbi su ne; Abdulkadir Mohammed Waziri (Akko LGA); Adamu Inuwa Pantami (Gombe); Mijinyawa Ardo Tilde (Funakaye); Mohammed Shettima Gadam (Kwami); Asma’u Iganus (Shongom); Mohammed Saidu Fawu (Billiri); da Salihu Baba Alkali (Nafada).

 

Sauran Kwamishinonin da ke zaman jiran tantancewa da sahalewarar Majalisar su ne Dr Barnabas Malle (Kaltungo), Dr Usman Maijama’a Kallamu (Kwami), Rtd. Lt. Col. Abdullahi Bello (Balanga), da Dr Abdullahi Bappah Garkuwa (Gombe).

 

Jim kadan bayan gabatar da jerin sunayen, kakakin Majalisar jihar ya sanar da tafiya hutun Majalisar na mako uku da za su dawo a ranar 21 ga watan Agustan.

 

Amma mako biyu bayan karewar wa’adin hutun da suka ce sun tafi, ‘yar yanzu ‘yan Majalisar ba su zauna domin fara aikin tantance Kwamishinonin da gwamnan ya aika musu ba.

 

Wani ma’aikacin Majalisar da ya nemi a sakaye sunansa ya shaida wa Daily Trust cewa gazawa wajen tantance Kwamishinonin bai rasa nasaba da rikicin da ke tsakanin majalisar dokoki da majalisar zatarwar jihar sakamakon ‘rashin biyansu alawus-alawus’.

 

Ya ce ‘yan majalisar a makon da ya gabata sun hadu, da nufin shawo kan rikicin domin ganin sun tantance Kwamishinon.

 

Sai dai daraktan yada labarai na majalisar, Abubakar Mohammed Umar, ya ce, ‘yan majalisar za su dawo zamansu a ranar Talata.

 

Ya tabbatar da cewa bayan dawowar nasu za su tantance kwamishinon da gwamnan ya tura musu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe
Labarai

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra
Labarai

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.