• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Majalisar Dokokin Gombe Ba Ta Tantance Kwamishinoni Ba

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Majalisar Dokokin jihar Gombe har yanzu ba ta tantance zababbun kwamishinoni 17 da gwamnan jihar Muhammadu Inuwa Yahaya ya tura mata ba, kwanaki 38 da suka wuce. 

 

A ranar 28 ga watan Yulin 2023 ne gwamna Inuwa Yahaya ya gabatar da jerin sunayen Kwamishinonin ga Majalisar Dokokin jihar, kwanaki 60 bayan rantsar da shi a matsayin gwamna karo na biyu kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanadar.

  • Rage Radadi: Gwamnatin Gombe Ta Amince Da Karin Albashin N10, 000 Ga Kowani Ma’aikaci

Sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, shi ne ya mika jerin sunayen ga akawun Majalisar Dokokin jihar, Barista Rukaiyatu A. Jalo, daga baya kakakin Majalisar, Abubakar Mohammed Luggerewo ya gabatar da sunayen a gaban kwaryar Majalisar.

Shida daga cikin zababbun Kwamishinonin sun yi aiki da Inuwa a zangonsa na farko su ne Dakta Habu Dahiru (Yamaltu/Deba), Barista Zubairu Mohammed Umar (Funakaye), Dr Aishatu Umar Maigari, Muhammad Gambo Magaji (Dukku), Alhaji Nasiru Mohammed Aliyu (Yamaltu/Deba) da Sanusi Ahmed Maidala (Akko), su na cikin zababbun mambobin majalisar zartaswa ta jihar 17.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

 

11 da suka kasance sabbi su ne; Abdulkadir Mohammed Waziri (Akko LGA); Adamu Inuwa Pantami (Gombe); Mijinyawa Ardo Tilde (Funakaye); Mohammed Shettima Gadam (Kwami); Asma’u Iganus (Shongom); Mohammed Saidu Fawu (Billiri); da Salihu Baba Alkali (Nafada).

 

Sauran Kwamishinonin da ke zaman jiran tantancewa da sahalewarar Majalisar su ne Dr Barnabas Malle (Kaltungo), Dr Usman Maijama’a Kallamu (Kwami), Rtd. Lt. Col. Abdullahi Bello (Balanga), da Dr Abdullahi Bappah Garkuwa (Gombe).

 

Jim kadan bayan gabatar da jerin sunayen, kakakin Majalisar jihar ya sanar da tafiya hutun Majalisar na mako uku da za su dawo a ranar 21 ga watan Agustan.

 

Amma mako biyu bayan karewar wa’adin hutun da suka ce sun tafi, ‘yar yanzu ‘yan Majalisar ba su zauna domin fara aikin tantance Kwamishinonin da gwamnan ya aika musu ba.

 

Wani ma’aikacin Majalisar da ya nemi a sakaye sunansa ya shaida wa Daily Trust cewa gazawa wajen tantance Kwamishinonin bai rasa nasaba da rikicin da ke tsakanin majalisar dokoki da majalisar zatarwar jihar sakamakon ‘rashin biyansu alawus-alawus’.

 

Ya ce ‘yan majalisar a makon da ya gabata sun hadu, da nufin shawo kan rikicin domin ganin sun tantance Kwamishinon.

 

Sai dai daraktan yada labarai na majalisar, Abubakar Mohammed Umar, ya ce, ‘yan majalisar za su dawo zamansu a ranar Talata.

 

Ya tabbatar da cewa bayan dawowar nasu za su tantance kwamishinon da gwamnan ya tura musu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version