• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Majalisar Dokokin Gombe Ba Ta Tantance Kwamishinoni Ba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Har Yanzu Majalisar Dokokin Gombe Ba Ta Tantance Kwamishinoni Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dokokin jihar Gombe har yanzu ba ta tantance zababbun kwamishinoni 17 da gwamnan jihar Muhammadu Inuwa Yahaya ya tura mata ba, kwanaki 38 da suka wuce. 

 

A ranar 28 ga watan Yulin 2023 ne gwamna Inuwa Yahaya ya gabatar da jerin sunayen Kwamishinonin ga Majalisar Dokokin jihar, kwanaki 60 bayan rantsar da shi a matsayin gwamna karo na biyu kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanadar.

  • Rage Radadi: Gwamnatin Gombe Ta Amince Da Karin Albashin N10, 000 Ga Kowani Ma’aikaci

Sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, shi ne ya mika jerin sunayen ga akawun Majalisar Dokokin jihar, Barista Rukaiyatu A. Jalo, daga baya kakakin Majalisar, Abubakar Mohammed Luggerewo ya gabatar da sunayen a gaban kwaryar Majalisar.

Shida daga cikin zababbun Kwamishinonin sun yi aiki da Inuwa a zangonsa na farko su ne Dakta Habu Dahiru (Yamaltu/Deba), Barista Zubairu Mohammed Umar (Funakaye), Dr Aishatu Umar Maigari, Muhammad Gambo Magaji (Dukku), Alhaji Nasiru Mohammed Aliyu (Yamaltu/Deba) da Sanusi Ahmed Maidala (Akko), su na cikin zababbun mambobin majalisar zartaswa ta jihar 17.

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

 

11 da suka kasance sabbi su ne; Abdulkadir Mohammed Waziri (Akko LGA); Adamu Inuwa Pantami (Gombe); Mijinyawa Ardo Tilde (Funakaye); Mohammed Shettima Gadam (Kwami); Asma’u Iganus (Shongom); Mohammed Saidu Fawu (Billiri); da Salihu Baba Alkali (Nafada).

 

Sauran Kwamishinonin da ke zaman jiran tantancewa da sahalewarar Majalisar su ne Dr Barnabas Malle (Kaltungo), Dr Usman Maijama’a Kallamu (Kwami), Rtd. Lt. Col. Abdullahi Bello (Balanga), da Dr Abdullahi Bappah Garkuwa (Gombe).

 

Jim kadan bayan gabatar da jerin sunayen, kakakin Majalisar jihar ya sanar da tafiya hutun Majalisar na mako uku da za su dawo a ranar 21 ga watan Agustan.

 

Amma mako biyu bayan karewar wa’adin hutun da suka ce sun tafi, ‘yar yanzu ‘yan Majalisar ba su zauna domin fara aikin tantance Kwamishinonin da gwamnan ya aika musu ba.

 

Wani ma’aikacin Majalisar da ya nemi a sakaye sunansa ya shaida wa Daily Trust cewa gazawa wajen tantance Kwamishinonin bai rasa nasaba da rikicin da ke tsakanin majalisar dokoki da majalisar zatarwar jihar sakamakon ‘rashin biyansu alawus-alawus’.

 

Ya ce ‘yan majalisar a makon da ya gabata sun hadu, da nufin shawo kan rikicin domin ganin sun tantance Kwamishinon.

 

Sai dai daraktan yada labarai na majalisar, Abubakar Mohammed Umar, ya ce, ‘yan majalisar za su dawo zamansu a ranar Talata.

 

Ya tabbatar da cewa bayan dawowar nasu za su tantance kwamishinon da gwamnan ya tura musu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijar Ta Sake Bude Sararin Samaniyarta Bayan Juyin Mulki

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

Related

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

2 minutes ago
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

1 hour ago
Labarai

AlÆ™alai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

4 hours ago
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
Labarai

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

5 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

7 hours ago
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta
Manyan Labarai

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

7 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

AlÆ™alai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.