ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Majalisar Dokokin Gombe Ba Ta Tantance Kwamishinoni Ba

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gombe

Majalisar Dokokin jihar Gombe har yanzu ba ta tantance zababbun kwamishinoni 17 da gwamnan jihar Muhammadu Inuwa Yahaya ya tura mata ba, kwanaki 38 da suka wuce. 

 

A ranar 28 ga watan Yulin 2023 ne gwamna Inuwa Yahaya ya gabatar da jerin sunayen Kwamishinonin ga Majalisar Dokokin jihar, kwanaki 60 bayan rantsar da shi a matsayin gwamna karo na biyu kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanadar.

ADVERTISEMENT
  • Rage Radadi: Gwamnatin Gombe Ta Amince Da Karin Albashin N10, 000 Ga Kowani Ma’aikaci

Sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, shi ne ya mika jerin sunayen ga akawun Majalisar Dokokin jihar, Barista Rukaiyatu A. Jalo, daga baya kakakin Majalisar, Abubakar Mohammed Luggerewo ya gabatar da sunayen a gaban kwaryar Majalisar.

Shida daga cikin zababbun Kwamishinonin sun yi aiki da Inuwa a zangonsa na farko su ne Dakta Habu Dahiru (Yamaltu/Deba), Barista Zubairu Mohammed Umar (Funakaye), Dr Aishatu Umar Maigari, Muhammad Gambo Magaji (Dukku), Alhaji Nasiru Mohammed Aliyu (Yamaltu/Deba) da Sanusi Ahmed Maidala (Akko), su na cikin zababbun mambobin majalisar zartaswa ta jihar 17.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

 

11 da suka kasance sabbi su ne; Abdulkadir Mohammed Waziri (Akko LGA); Adamu Inuwa Pantami (Gombe); Mijinyawa Ardo Tilde (Funakaye); Mohammed Shettima Gadam (Kwami); Asma’u Iganus (Shongom); Mohammed Saidu Fawu (Billiri); da Salihu Baba Alkali (Nafada).

 

Sauran Kwamishinonin da ke zaman jiran tantancewa da sahalewarar Majalisar su ne Dr Barnabas Malle (Kaltungo), Dr Usman Maijama’a Kallamu (Kwami), Rtd. Lt. Col. Abdullahi Bello (Balanga), da Dr Abdullahi Bappah Garkuwa (Gombe).

 

Jim kadan bayan gabatar da jerin sunayen, kakakin Majalisar jihar ya sanar da tafiya hutun Majalisar na mako uku da za su dawo a ranar 21 ga watan Agustan.

 

Amma mako biyu bayan karewar wa’adin hutun da suka ce sun tafi, ‘yar yanzu ‘yan Majalisar ba su zauna domin fara aikin tantance Kwamishinonin da gwamnan ya aika musu ba.

 

Wani ma’aikacin Majalisar da ya nemi a sakaye sunansa ya shaida wa Daily Trust cewa gazawa wajen tantance Kwamishinonin bai rasa nasaba da rikicin da ke tsakanin majalisar dokoki da majalisar zatarwar jihar sakamakon ‘rashin biyansu alawus-alawus’.

 

Ya ce ‘yan majalisar a makon da ya gabata sun hadu, da nufin shawo kan rikicin domin ganin sun tantance Kwamishinon.

 

Sai dai daraktan yada labarai na majalisar, Abubakar Mohammed Umar, ya ce, ‘yan majalisar za su dawo zamansu a ranar Talata.

 

Ya tabbatar da cewa bayan dawowar nasu za su tantance kwamishinon da gwamnan ya tura musu.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Roki NLC Da Ta Janye Shirin Tsunduma Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.