• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-haren Boko Haram Biyu Sun Yi Ta’adi A Borno

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Hare-haren Boko Haram Biyu Sun Yi Ta’adi A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar ‘yan ta’adda ta Boko Haram ta kai wasu hare-hare guda biyu a ranar Lahadin da ta gabata da kuma ranar Talatar makon nan inda suka yi ta’adi a Jihar Borno.

Hari na farko da suka kai a daren Lahadi a ofishin ‘yansanda na Jakana da ke Karamar Hukumar Konduga a Jihar Borno, ya yi sanadin mutuwar wani direban ‘yansanda da wata mata.

  • An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano
  • Zanga-zanga: Kungiya Ta Gudanar Zanga-zangar Lumana A Jihar Filato

Maharan sun kuma kona motocin sintiri guda biyu na ‘yansanda da na ‘yan sa kai (CJTF), tare da wani babur, sannan suka sace makamai da alburusai.

Jakana, tana da tazarar kilomita 45 daga Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, a kan babbar hanyar Damaturu zuwa Maiduguri.

A cewar majiyoyin yankin, ‘yan ta’addan sun kai harin ne da misalin karfe 1 na dare, inda suka yi artabu da jami’an tsaro a wani kazamin fadan da ya dauki tsawon sa’oi kusan uku ana gwabzawa. Daga karshe ‘yan ta’addan suka ci karfin jami’an tsaron.

Labarai Masu Nasaba

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

Shugaban karamar hukumar Konduga, Hon. Abbas Ali Abari, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da wakilin LEADERSHIP.

A hari na biyu kuma a ranar Talata, ‘yan ta’addan sun kashe wani babban akanta na sashen ilimi a Karamar Hukumar Damboa da ke Jihar Borno, Shettima Mustapha yayin da wani bom da suka dasa a kan hanya ya fashe.

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, wani abokin marigayi Mustapaha da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce, “tabbas akantanmu mutumin kirki, Shettima Mustapha ya rasu a wani harin bom yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Maiduguri daga Damboa a yau (Talata).

“Muna cike da jimamin wannan babban rashi kuma muna mika ta’aziyyarmu ga iyalansa da sauran ‘yan uwa. Allah ya rahamshe shi”.

Bom din ya kuma raunata wasu mutane da motarsu ta bi ta kai cikin rashin sani.

Majiya da dama sun bayyana cewa al’amarin ya auku ne da rana tsaka a ranar Talatar yayin da sojoji da sauran jami’an tsaro suke rakiyar daruruwan masu ababen hawa daga Damboa zuwa Maiduguri.

Wadannan hare-hare dai sun kara tayar da hankulan mutane tun bayan wadanda wasu ‘yan mata masu kunar bakin wake suka kai a Karamar Hukumar Gwoza da ke Jihar Borno, kimanin wata daya da ya gabata, inda suka kashe akalla mutum 42 da kuma raunata wasu 100.

Hanyar Maiduguri zuwa Damboa dai ta zama tarkon mutuwa bayan wasu munanan hare-haren da ‘yan ta’adda suka kai da suka yi sanadin kashe mutane da dama kafin lokacin da sojojin suka sake bude hanyar don bai wa al’ummar Damboa da wasu sassa na Chibok damar zuwa Maiduguri ta hanyar, yayin da su kuma mutanen Biu sai sun bi ta Buni Yadi zuwa Damaturu tsawon kilomita 300 kafin su isa Maiduguri, babban birnin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BarnaBoko HaramBornoHari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Zanga-Zanga Sun Ƙona Ofisoshin Ƴansanda, Sun Kashe Babban Jami’i

Next Post

Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

Related

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

42 minutes ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

2 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

2 hours ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

2 hours ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 hours ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

3 hours ago
Next Post
Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

LABARAI MASU NASABA

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

September 5, 2025
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

September 5, 2025
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

September 5, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

September 5, 2025
'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

September 5, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.