• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-haren Boko Haram Biyu Sun Yi Ta’adi A Borno

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Boko Haram

Kungiyar ‘yan ta’adda ta Boko Haram ta kai wasu hare-hare guda biyu a ranar Lahadin da ta gabata da kuma ranar Talatar makon nan inda suka yi ta’adi a Jihar Borno.

Hari na farko da suka kai a daren Lahadi a ofishin ‘yansanda na Jakana da ke Karamar Hukumar Konduga a Jihar Borno, ya yi sanadin mutuwar wani direban ‘yansanda da wata mata.

  • An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano
  • Zanga-zanga: Kungiya Ta Gudanar Zanga-zangar Lumana A Jihar Filato

Maharan sun kuma kona motocin sintiri guda biyu na ‘yansanda da na ‘yan sa kai (CJTF), tare da wani babur, sannan suka sace makamai da alburusai.

Jakana, tana da tazarar kilomita 45 daga Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, a kan babbar hanyar Damaturu zuwa Maiduguri.

A cewar majiyoyin yankin, ‘yan ta’addan sun kai harin ne da misalin karfe 1 na dare, inda suka yi artabu da jami’an tsaro a wani kazamin fadan da ya dauki tsawon sa’oi kusan uku ana gwabzawa. Daga karshe ‘yan ta’addan suka ci karfin jami’an tsaron.

LABARAI MASU NASABA

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

Shugaban karamar hukumar Konduga, Hon. Abbas Ali Abari, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da wakilin LEADERSHIP.

A hari na biyu kuma a ranar Talata, ‘yan ta’addan sun kashe wani babban akanta na sashen ilimi a Karamar Hukumar Damboa da ke Jihar Borno, Shettima Mustapha yayin da wani bom da suka dasa a kan hanya ya fashe.

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, wani abokin marigayi Mustapaha da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce, “tabbas akantanmu mutumin kirki, Shettima Mustapha ya rasu a wani harin bom yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Maiduguri daga Damboa a yau (Talata).

“Muna cike da jimamin wannan babban rashi kuma muna mika ta’aziyyarmu ga iyalansa da sauran ‘yan uwa. Allah ya rahamshe shi”.

Bom din ya kuma raunata wasu mutane da motarsu ta bi ta kai cikin rashin sani.

Majiya da dama sun bayyana cewa al’amarin ya auku ne da rana tsaka a ranar Talatar yayin da sojoji da sauran jami’an tsaro suke rakiyar daruruwan masu ababen hawa daga Damboa zuwa Maiduguri.

Wadannan hare-hare dai sun kara tayar da hankulan mutane tun bayan wadanda wasu ‘yan mata masu kunar bakin wake suka kai a Karamar Hukumar Gwoza da ke Jihar Borno, kimanin wata daya da ya gabata, inda suka kashe akalla mutum 42 da kuma raunata wasu 100.

Hanyar Maiduguri zuwa Damboa dai ta zama tarkon mutuwa bayan wasu munanan hare-haren da ‘yan ta’adda suka kai da suka yi sanadin kashe mutane da dama kafin lokacin da sojojin suka sake bude hanyar don bai wa al’ummar Damboa da wasu sassa na Chibok damar zuwa Maiduguri ta hanyar, yayin da su kuma mutanen Biu sai sun bi ta Buni Yadi zuwa Damaturu tsawon kilomita 300 kafin su isa Maiduguri, babban birnin jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Labarai

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
Next Post
Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.