• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-haren Boko Haram Biyu Sun Yi Ta’adi A Borno

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Labarai
0
Hare-haren Boko Haram Biyu Sun Yi Ta’adi A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar ‘yan ta’adda ta Boko Haram ta kai wasu hare-hare guda biyu a ranar Lahadin da ta gabata da kuma ranar Talatar makon nan inda suka yi ta’adi a Jihar Borno.

Hari na farko da suka kai a daren Lahadi a ofishin ‘yansanda na Jakana da ke Karamar Hukumar Konduga a Jihar Borno, ya yi sanadin mutuwar wani direban ‘yansanda da wata mata.

  • An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano
  • Zanga-zanga: Kungiya Ta Gudanar Zanga-zangar Lumana A Jihar Filato

Maharan sun kuma kona motocin sintiri guda biyu na ‘yansanda da na ‘yan sa kai (CJTF), tare da wani babur, sannan suka sace makamai da alburusai.

Jakana, tana da tazarar kilomita 45 daga Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, a kan babbar hanyar Damaturu zuwa Maiduguri.

A cewar majiyoyin yankin, ‘yan ta’addan sun kai harin ne da misalin karfe 1 na dare, inda suka yi artabu da jami’an tsaro a wani kazamin fadan da ya dauki tsawon sa’oi kusan uku ana gwabzawa. Daga karshe ‘yan ta’addan suka ci karfin jami’an tsaron.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Shugaban karamar hukumar Konduga, Hon. Abbas Ali Abari, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da wakilin LEADERSHIP.

A hari na biyu kuma a ranar Talata, ‘yan ta’addan sun kashe wani babban akanta na sashen ilimi a Karamar Hukumar Damboa da ke Jihar Borno, Shettima Mustapha yayin da wani bom da suka dasa a kan hanya ya fashe.

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, wani abokin marigayi Mustapaha da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce, “tabbas akantanmu mutumin kirki, Shettima Mustapha ya rasu a wani harin bom yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Maiduguri daga Damboa a yau (Talata).

“Muna cike da jimamin wannan babban rashi kuma muna mika ta’aziyyarmu ga iyalansa da sauran ‘yan uwa. Allah ya rahamshe shi”.

Bom din ya kuma raunata wasu mutane da motarsu ta bi ta kai cikin rashin sani.

Majiya da dama sun bayyana cewa al’amarin ya auku ne da rana tsaka a ranar Talatar yayin da sojoji da sauran jami’an tsaro suke rakiyar daruruwan masu ababen hawa daga Damboa zuwa Maiduguri.

Wadannan hare-hare dai sun kara tayar da hankulan mutane tun bayan wadanda wasu ‘yan mata masu kunar bakin wake suka kai a Karamar Hukumar Gwoza da ke Jihar Borno, kimanin wata daya da ya gabata, inda suka kashe akalla mutum 42 da kuma raunata wasu 100.

Hanyar Maiduguri zuwa Damboa dai ta zama tarkon mutuwa bayan wasu munanan hare-haren da ‘yan ta’adda suka kai da suka yi sanadin kashe mutane da dama kafin lokacin da sojojin suka sake bude hanyar don bai wa al’ummar Damboa da wasu sassa na Chibok damar zuwa Maiduguri ta hanyar, yayin da su kuma mutanen Biu sai sun bi ta Buni Yadi zuwa Damaturu tsawon kilomita 300 kafin su isa Maiduguri, babban birnin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BarnaBoko HaramBornoHari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Zanga-Zanga Sun Ƙona Ofisoshin Ƴansanda, Sun Kashe Babban Jami’i

Next Post

Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

4 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

5 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

7 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

9 hours ago
Next Post
Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.