• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-haren Boko Haram Biyu Sun Yi Ta’adi A Borno

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Labarai
0
Hare-haren Boko Haram Biyu Sun Yi Ta’adi A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar ‘yan ta’adda ta Boko Haram ta kai wasu hare-hare guda biyu a ranar Lahadin da ta gabata da kuma ranar Talatar makon nan inda suka yi ta’adi a Jihar Borno.

Hari na farko da suka kai a daren Lahadi a ofishin ‘yansanda na Jakana da ke Karamar Hukumar Konduga a Jihar Borno, ya yi sanadin mutuwar wani direban ‘yansanda da wata mata.

  • An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano
  • Zanga-zanga: Kungiya Ta Gudanar Zanga-zangar Lumana A Jihar Filato

Maharan sun kuma kona motocin sintiri guda biyu na ‘yansanda da na ‘yan sa kai (CJTF), tare da wani babur, sannan suka sace makamai da alburusai.

Jakana, tana da tazarar kilomita 45 daga Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, a kan babbar hanyar Damaturu zuwa Maiduguri.

A cewar majiyoyin yankin, ‘yan ta’addan sun kai harin ne da misalin karfe 1 na dare, inda suka yi artabu da jami’an tsaro a wani kazamin fadan da ya dauki tsawon sa’oi kusan uku ana gwabzawa. Daga karshe ‘yan ta’addan suka ci karfin jami’an tsaron.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Shugaban karamar hukumar Konduga, Hon. Abbas Ali Abari, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da wakilin LEADERSHIP.

A hari na biyu kuma a ranar Talata, ‘yan ta’addan sun kashe wani babban akanta na sashen ilimi a Karamar Hukumar Damboa da ke Jihar Borno, Shettima Mustapha yayin da wani bom da suka dasa a kan hanya ya fashe.

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, wani abokin marigayi Mustapaha da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce, “tabbas akantanmu mutumin kirki, Shettima Mustapha ya rasu a wani harin bom yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Maiduguri daga Damboa a yau (Talata).

“Muna cike da jimamin wannan babban rashi kuma muna mika ta’aziyyarmu ga iyalansa da sauran ‘yan uwa. Allah ya rahamshe shi”.

Bom din ya kuma raunata wasu mutane da motarsu ta bi ta kai cikin rashin sani.

Majiya da dama sun bayyana cewa al’amarin ya auku ne da rana tsaka a ranar Talatar yayin da sojoji da sauran jami’an tsaro suke rakiyar daruruwan masu ababen hawa daga Damboa zuwa Maiduguri.

Wadannan hare-hare dai sun kara tayar da hankulan mutane tun bayan wadanda wasu ‘yan mata masu kunar bakin wake suka kai a Karamar Hukumar Gwoza da ke Jihar Borno, kimanin wata daya da ya gabata, inda suka kashe akalla mutum 42 da kuma raunata wasu 100.

Hanyar Maiduguri zuwa Damboa dai ta zama tarkon mutuwa bayan wasu munanan hare-haren da ‘yan ta’adda suka kai da suka yi sanadin kashe mutane da dama kafin lokacin da sojojin suka sake bude hanyar don bai wa al’ummar Damboa da wasu sassa na Chibok damar zuwa Maiduguri ta hanyar, yayin da su kuma mutanen Biu sai sun bi ta Buni Yadi zuwa Damaturu tsawon kilomita 300 kafin su isa Maiduguri, babban birnin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BarnaBoko HaramBornoHari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Zanga-Zanga Sun Ƙona Ofisoshin Ƴansanda, Sun Kashe Babban Jami’i

Next Post

Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

14 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

14 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

15 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

15 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

18 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

19 hours ago
Next Post
Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.