• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-haren ‘Yan Bindiga A Sahel Sun Jefa Shugabannin Soji Cikin Zulumi

by Rabi'u Ali Indabawa, Muhammad and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Hare-haren ‘Yan Bindiga A Sahel Sun Jefa Shugabannin Soji Cikin Zulumi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tutar kungiyar al-Ka’ida na kadawa a filin jirgin sama bayan wasu ‘yanbindiga sun jefa tsimma mai ci da wuta a cikin injin jirgin sama, wasu kuma suka fantsama sashen alfarma na filin jirgin suna harbe-harbe lokacin da suka nufi wani jirgin hukumar ba da tallafi na Majalisar Dinkin Duniya (UNHAS).

 

Hotunan da aka dinga yadawa na maharan da suka kai farmaki ranar 17 ga watan Satumba kan filin jirgin sama na Birnin Bamako da ke Mali, sun fito da matsalar tsaro fili a wurin da ya kamata a ce na cikin mafiya tsaro a yankin Afirka ta Yamma.

  • Akwai Bukatar Shugabannin Arewa Su Farka – Sarkin Fawa
  • Xi Ya Yi Kira Ga Ma’aikatan Masana’antu Da Su Ba Da Gudummawar Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin

An kuma kai wa cibiyar horarwa ta jami’an tsaron Gendarmerie hari da ke yankin Faladié. Mazauna yankin sun dauki bidiyon yadda hayaki ke tashi daidai lokacin da ake jin karar tashin bamabamai da harbe-harbe.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

Wani bidiyon ‘yanbindigar da ya tayar da hankali kuma shi ne wanda aka ga mahara masu kananan shekaru na kintsa kansu kafin kai har-haren.

 

Sojojin da ke mulkin Mali ba su bayyana mutanen da aka kashe ba a harin, kawai dai an ce wasu jami’an tsaron sun rasa rayukansu.

 

Amma da alama mutanen da suka mutu za su kai 80 zuwa 100 tare da raunata wasu 200 ko fiye.

 

Adadin ka iya kunsa ko akasin haka na maharan, kuma tuni dakarun gwamnati suka sake kwace iko da filin jirgin da ke Senou, da kuma barikin Faladie.

 

Kasar ta afka rikici ne tun daga 2011, lokacin da ‘yan kabilar Abzinawa masu neman ballewa suka hada kai da masu ikirarin Jihadi kuma suka kwace iko da Binrin Timbuktu, da Gao, da sauran garuruwan da ke Arewacin kasar.

 

An sha kai wa Birnin Bamako hare-hare a baya. A 2015, wani hari kan otel din Radisson Blu ya yi sanadiyyar kashe mutum 20, sannan wasu biyar suka mutu a harbe-harben da aka yi a wani wurin cin abinci na unguwar Hippodrome.

 

A 2017, hari kan wurin yawon bude-ido da ke wajen birnin ya kashe akalla mutum hudu.
A 2020, Kanar Assimi Goita, wani kwamandan yaki, ya jagoranci juyin mulki kan zababbiyar gwamnati saboda zarginta da gazawa wajen kawo karshen matsalar tsaron.

 

Daga baya aka kafa gwamnatin rikon kwarya, amma a watan Mayun 2021 Kanar Goita ya sake jagorantar juyin mulkin, inda ya kafa kansa da abokan aikinsa a matsayin jagorori.

 

Amma duk da mayar da hankali kan taro da kuma daukar hayar dakarun haya na Rasha mai suna Wagner don taimaka wa sojojin kasar wanda ya jawo lalacewar alaka da Faransa da kuma korar dubban sojojin kasar daga Mali masu mulkin yanzu ba su fi gwamnatin da suka gada kokari ba.

 

An fi fafata yakin a yankunan sahara da ke Arewacin kasar, da kuma tsakiyar kasar, inda ake yawan samun rikici tsakanin manoma na kabilar Dogon da kuma makiyayan kabilar Peul (Fulani) game da kasa da kuma ruwan sha na kiwo.

 

Sai dai kuma a watan Yulin 2022 masu ikirarin jihadi sun kai hare-hare biyu a kusa da garin da zimmar auka wa barikin soja na Kati da ke da nisan kilomita 15 kacal daga Bamako.

 

Sai dai dakarun gwamnati sun yi nasarar dakile harin suna cewa ‘yanbindiga biyu kawai aka kashe a harin. An alakanta harin da kungiyar Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM), wacce ita ce mafi girma a kasar mai alaka da al-Ka’ida.

 

‘Yan makonni bayan nan kuma Faransa ta kammala kwashe sojojinta bayan gwamnatin sojin ta kore su. Daga nan kuma, sai suka nemi dakarun Majalisar Dinkin Duniya su fice daga 14,000 su fita daga kasar.

 

Saboda haka, ko gwamnatin Goita za ta iya hofantar da harin da aka yada wa duniya kamar yadda ta yi bayan harin Yulin 2022?
Yanayin tsaro a Afirka ta Yamma ya sha bamban da na 2022.

 

A yankin tsakiyar Sahel, kungiyar JNIM da sauran masu ikirarin jihadi kamar Islamic State in the Greater Sahara (ISGS), na ci gaba da nausawa Kudanci.

 

Gwamnatin soja ta Burkina Faso mai makobtaka da ke kawance da Mali da Nijar a kawancen Alliance of Sahelian States (AES), ita ma ta rasa iko da yankuna da dama, musamman a yankunan karkara.

 

A Nijar ma, ‘yanbindigar na ci gaba da kai hare-hare a Yammaci, har ma da kusa da Yamai babban birnin kasar.

 

Bugu da kari, yanzu maharan kan nausa zuwa Arewacin kasashen kuma kusa da Togo da Benin. A Ivory Coast, an dakile su ne sakamakon kokarin sojin kasar da kuma ayyukan raya kasa da gwamnati ke yi.

 

Saboda haka yanayin tsaro a yankin yanzu ya tsananta sama da kowane lokaci a baya.
Sai dai lamarin ya dan sha bamban a Mali.

 

A shekarar da ta gabata dakarun gwamnati suka yi nasarar kwace garuruwan Arewaci da ke hannun Abzinawa, wadanda suka saka hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin farar hula a 2015 amma kuma sojojin suka soke.

 

Duk da cewa mayakan sun bai wa dakarun Mali da abokansu na Wagner wahala a Tinzaouaten da ke cikin rairayin Sahara, har yanzu gwanatin ce ke rike da ikon biranen yankin.

 

Wannan kokari na kwato wurare kamar Kidal ya farfado da farin jinin gwamnatin a zukatan jama’ar Bamako.

 

Cikin abubuwan da suka faru bayan harin, mun ga yadda aka kama wasu mutane da zargin hannunsu, da kuma wani mutum aka kona da ransa a kan titi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Uwargida Za Ta Hada Tsimin Sassaken Baure

Next Post

Bani Da Wani Buri A Yanzu Da Ya Wuce In Ganni A Dakin Mijina – Khadija Muhammad

Related

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

56 minutes ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

2 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

4 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

6 hours ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

6 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

8 hours ago
Next Post
Bani Da Wani Buri A Yanzu Da Ya Wuce In Ganni A Dakin Mijina – Khadija Muhammad

Bani Da Wani Buri A Yanzu Da Ya Wuce In Ganni A Dakin Mijina - Khadija Muhammad

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.