ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-haren ‘Yan Bindiga A Sahel Sun Jefa Shugabannin Soji Cikin Zulumi

by Rabi'u Ali Indabawa, Muhammad and Sulaiman
2 years ago
Sahel

Tutar kungiyar al-Ka’ida na kadawa a filin jirgin sama bayan wasu ‘yanbindiga sun jefa tsimma mai ci da wuta a cikin injin jirgin sama, wasu kuma suka fantsama sashen alfarma na filin jirgin suna harbe-harbe lokacin da suka nufi wani jirgin hukumar ba da tallafi na Majalisar Dinkin Duniya (UNHAS).

 

Hotunan da aka dinga yadawa na maharan da suka kai farmaki ranar 17 ga watan Satumba kan filin jirgin sama na Birnin Bamako da ke Mali, sun fito da matsalar tsaro fili a wurin da ya kamata a ce na cikin mafiya tsaro a yankin Afirka ta Yamma.

ADVERTISEMENT
  • Akwai Bukatar Shugabannin Arewa Su Farka – Sarkin Fawa
  • Xi Ya Yi Kira Ga Ma’aikatan Masana’antu Da Su Ba Da Gudummawar Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin

An kuma kai wa cibiyar horarwa ta jami’an tsaron Gendarmerie hari da ke yankin Faladié. Mazauna yankin sun dauki bidiyon yadda hayaki ke tashi daidai lokacin da ake jin karar tashin bamabamai da harbe-harbe.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Wani bidiyon ‘yanbindigar da ya tayar da hankali kuma shi ne wanda aka ga mahara masu kananan shekaru na kintsa kansu kafin kai har-haren.

 

Sojojin da ke mulkin Mali ba su bayyana mutanen da aka kashe ba a harin, kawai dai an ce wasu jami’an tsaron sun rasa rayukansu.

 

Amma da alama mutanen da suka mutu za su kai 80 zuwa 100 tare da raunata wasu 200 ko fiye.

 

Adadin ka iya kunsa ko akasin haka na maharan, kuma tuni dakarun gwamnati suka sake kwace iko da filin jirgin da ke Senou, da kuma barikin Faladie.

 

Kasar ta afka rikici ne tun daga 2011, lokacin da ‘yan kabilar Abzinawa masu neman ballewa suka hada kai da masu ikirarin Jihadi kuma suka kwace iko da Binrin Timbuktu, da Gao, da sauran garuruwan da ke Arewacin kasar.

 

An sha kai wa Birnin Bamako hare-hare a baya. A 2015, wani hari kan otel din Radisson Blu ya yi sanadiyyar kashe mutum 20, sannan wasu biyar suka mutu a harbe-harben da aka yi a wani wurin cin abinci na unguwar Hippodrome.

 

A 2017, hari kan wurin yawon bude-ido da ke wajen birnin ya kashe akalla mutum hudu.
A 2020, Kanar Assimi Goita, wani kwamandan yaki, ya jagoranci juyin mulki kan zababbiyar gwamnati saboda zarginta da gazawa wajen kawo karshen matsalar tsaron.

 

Daga baya aka kafa gwamnatin rikon kwarya, amma a watan Mayun 2021 Kanar Goita ya sake jagorantar juyin mulkin, inda ya kafa kansa da abokan aikinsa a matsayin jagorori.

 

Amma duk da mayar da hankali kan taro da kuma daukar hayar dakarun haya na Rasha mai suna Wagner don taimaka wa sojojin kasar wanda ya jawo lalacewar alaka da Faransa da kuma korar dubban sojojin kasar daga Mali masu mulkin yanzu ba su fi gwamnatin da suka gada kokari ba.

 

An fi fafata yakin a yankunan sahara da ke Arewacin kasar, da kuma tsakiyar kasar, inda ake yawan samun rikici tsakanin manoma na kabilar Dogon da kuma makiyayan kabilar Peul (Fulani) game da kasa da kuma ruwan sha na kiwo.

 

Sai dai kuma a watan Yulin 2022 masu ikirarin jihadi sun kai hare-hare biyu a kusa da garin da zimmar auka wa barikin soja na Kati da ke da nisan kilomita 15 kacal daga Bamako.

 

Sai dai dakarun gwamnati sun yi nasarar dakile harin suna cewa ‘yanbindiga biyu kawai aka kashe a harin. An alakanta harin da kungiyar Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM), wacce ita ce mafi girma a kasar mai alaka da al-Ka’ida.

 

‘Yan makonni bayan nan kuma Faransa ta kammala kwashe sojojinta bayan gwamnatin sojin ta kore su. Daga nan kuma, sai suka nemi dakarun Majalisar Dinkin Duniya su fice daga 14,000 su fita daga kasar.

 

Saboda haka, ko gwamnatin Goita za ta iya hofantar da harin da aka yada wa duniya kamar yadda ta yi bayan harin Yulin 2022?
Yanayin tsaro a Afirka ta Yamma ya sha bamban da na 2022.

 

A yankin tsakiyar Sahel, kungiyar JNIM da sauran masu ikirarin jihadi kamar Islamic State in the Greater Sahara (ISGS), na ci gaba da nausawa Kudanci.

 

Gwamnatin soja ta Burkina Faso mai makobtaka da ke kawance da Mali da Nijar a kawancen Alliance of Sahelian States (AES), ita ma ta rasa iko da yankuna da dama, musamman a yankunan karkara.

 

A Nijar ma, ‘yanbindigar na ci gaba da kai hare-hare a Yammaci, har ma da kusa da Yamai babban birnin kasar.

 

Bugu da kari, yanzu maharan kan nausa zuwa Arewacin kasashen kuma kusa da Togo da Benin. A Ivory Coast, an dakile su ne sakamakon kokarin sojin kasar da kuma ayyukan raya kasa da gwamnati ke yi.

 

Saboda haka yanayin tsaro a yankin yanzu ya tsananta sama da kowane lokaci a baya.
Sai dai lamarin ya dan sha bamban a Mali.

 

A shekarar da ta gabata dakarun gwamnati suka yi nasarar kwace garuruwan Arewaci da ke hannun Abzinawa, wadanda suka saka hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin farar hula a 2015 amma kuma sojojin suka soke.

 

Duk da cewa mayakan sun bai wa dakarun Mali da abokansu na Wagner wahala a Tinzaouaten da ke cikin rairayin Sahara, har yanzu gwanatin ce ke rike da ikon biranen yankin.

 

Wannan kokari na kwato wurare kamar Kidal ya farfado da farin jinin gwamnatin a zukatan jama’ar Bamako.

 

Cikin abubuwan da suka faru bayan harin, mun ga yadda aka kama wasu mutane da zargin hannunsu, da kuma wani mutum aka kona da ransa a kan titi.

Sahel
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
Sahel
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje
Sahel
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Bani Da Wani Buri A Yanzu Da Ya Wuce In Ganni A Dakin Mijina – Khadija Muhammad

Bani Da Wani Buri A Yanzu Da Ya Wuce In Ganni A Dakin Mijina - Khadija Muhammad

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.