ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Cocin Kafanchan: Wasu Ne Ke Yunƙurin Kitsa Rikicin Addini, Za Mu Damƙo Su – Uba Sani

by Sulaiman
2 years ago
Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Mai Girma Sanata Uba Sani, ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin da aka kai a cocin Fadan Kamatan- Katolika na Kafanchan, da ke karamar hukumar Zangon Kataf a jihar Kaduna.

Da yake nuna bacin ransa game da harin a ranar 8 ga watan Satumba wanda ya yi sanadin asarar rayuka, Gwamnan ya sha alwashin zakulo wadanda suka aikata wannan mummunan aikin tare da tabbatar da cewa sun fuskanci tsantsar fushin doka. Ya ce an kai harin ne da nufin tayar da rikicin kabilanci da addini a jihar Kaduna da kuma zagon kasa ga kokarin gwamnati na sake dawo da aminci tsakanin al’ummar jihar.

  • Gwamna Uba Sani Ya Amince A Biya Likitoci Kashi 100 Na Sabon Tsarin Albashinsu

Gwamna Uba Sani ya bukaci jami’an tsaro da su gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da tabbatar da kama wadanda ke da hannu cikin kai harin.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya jajanta wa iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su tare da ba su tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta tallafa musu kan wannan mawuyaciyar rayuwa da ake ciki a wannan lokaci.

Gwamnatin Gwamna Uba Sani ta dauki kwararan matakai na maido da zaman lafiya a cikin al’ummomin da ke fama da rikici ta hanyar karfafa hadin guiwa da Hukumomin Tsaro na Tarayya da kuma karfafa hukumar ‘yan banga ta Kaduna (KADVS). Kwanan nan ne gwamnatin jihar ta dauki sabbin jami’an tsaro na ‘yan banga 7,000 tare da horar da su.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Gwamnatin Kaduna ta kuma gudanar da muhimman tsare-tsare kan harkokin tsaro inda ta tattauna da manyan jami’an gwamnatin tarayya da ke da alhakin tsaro kamar ministan harkokin ‘yansanda, Sanata Ibrahim Geidam; Karamin ministan harkokin ‘yansanda, Hon. Imaan Sulaiman-Ibrahim da shugabannin tsaro da aka nada kwanan nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai

Shirin Tinubu Na Samar Da Tabarau Miliyan Biyar Ga Masu Fama Da Ciwon Ido

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.