• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Cocin Kafanchan: Wasu Ne Ke Yunƙurin Kitsa Rikicin Addini, Za Mu Damƙo Su – Uba Sani

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Mai Girma Sanata Uba Sani, ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin da aka kai a cocin Fadan Kamatan- Katolika na Kafanchan, da ke karamar hukumar Zangon Kataf a jihar Kaduna.

Da yake nuna bacin ransa game da harin a ranar 8 ga watan Satumba wanda ya yi sanadin asarar rayuka, Gwamnan ya sha alwashin zakulo wadanda suka aikata wannan mummunan aikin tare da tabbatar da cewa sun fuskanci tsantsar fushin doka. Ya ce an kai harin ne da nufin tayar da rikicin kabilanci da addini a jihar Kaduna da kuma zagon kasa ga kokarin gwamnati na sake dawo da aminci tsakanin al’ummar jihar.

  • Gwamna Uba Sani Ya Amince A Biya Likitoci Kashi 100 Na Sabon Tsarin Albashinsu

Gwamna Uba Sani ya bukaci jami’an tsaro da su gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da tabbatar da kama wadanda ke da hannu cikin kai harin.

Gwamnan ya jajanta wa iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su tare da ba su tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta tallafa musu kan wannan mawuyaciyar rayuwa da ake ciki a wannan lokaci.

Gwamnatin Gwamna Uba Sani ta dauki kwararan matakai na maido da zaman lafiya a cikin al’ummomin da ke fama da rikici ta hanyar karfafa hadin guiwa da Hukumomin Tsaro na Tarayya da kuma karfafa hukumar ‘yan banga ta Kaduna (KADVS). Kwanan nan ne gwamnatin jihar ta dauki sabbin jami’an tsaro na ‘yan banga 7,000 tare da horar da su.

Labarai Masu Nasaba

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Gwamnatin Kaduna ta kuma gudanar da muhimman tsare-tsare kan harkokin tsaro inda ta tattauna da manyan jami’an gwamnatin tarayya da ke da alhakin tsaro kamar ministan harkokin ‘yansanda, Sanata Ibrahim Geidam; Karamin ministan harkokin ‘yansanda, Hon. Imaan Sulaiman-Ibrahim da shugabannin tsaro da aka nada kwanan nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CociKadunaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Yobe A Shekara 32 Da Kafuwa: Ci Gaba Da Koma-bayanta

Next Post

Shirin Tinubu Na Samar Da Tabarau Miliyan Biyar Ga Masu Fama Da Ciwon Ido

Related

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

1 hour ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

4 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

5 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

5 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

6 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

8 hours ago
Next Post
Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai

Shirin Tinubu Na Samar Da Tabarau Miliyan Biyar Ga Masu Fama Da Ciwon Ido

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.