ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Jirgin Kasan Kaduna-Abuja: Gwamnatin Neja Ta Bukaci A Saki Matar Tsohon Gwamnan Kano Da ‘Ya’ya 5

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Gwamnatin Neja

Gwamnatin jihar Neja ta yunkuro domin tabbatar da an ceto mata da ‘ya’yan tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jigo a jam’iyyar APC, Janar Idris Garba daga hannun masu garkuwa da mutane wadanda harin Jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja ya shafa.

An sace matar tsohon gwamnan Maryam Bobbo, da ‘ya’yansa maza Abubakar da Ibrahim Idris Garba da kuma ‘ya’yansa uku Fatima, Imran da Zainab duk an yi garkuwa da su.

  • Tarayyar Turai Za Ta Yi Nazari Kan Lafta Wa Rasha Karin Takunkumai
  • An Dakatar Da Sarkin Da Ya Yi Wa Kasurgumin Dan Bindiga Sarauta A Zamfara

Sakataren Gwamnatin jihar Neja, Ahmed Ibrahim Matane, ne ya jagoranci tawagar gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello zuwa gidan tsohon gwamnan Kano, Wazirin Lapai kuma shugaban Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida a karshen mako.

ADVERTISEMENT

Da ya ke misalta lamarin a matsayin abun tir da kaico na yin garkuwa da iyalansa har mutum shida, ya ce, harin jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja ya sake farkar da gwamantin Neja kan yaki da ‘yan ta’adda.

Ya roki iyalan Wazirin Lapai da sauran wadanda aka yi garkuwa da ahalinsu da su ji kwarin guiwa daga bangaren gwamnati na cewa ita gwamnatin za ta yi dukkanin mai yiyuwa wajen ganin iyalansu sun kubuta daga hannun ‘yan ta’addan.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Ya fada wa shugaban IBBU wakilan gwamnatin Neja, sun ziyarci gidansa ne domin tabbatar masa da cewa gwamantin jihar a kan kafafunta take wajen yaki da ‘yan ta’adda da tabbatar da cafke su a kowane lokaci.

Matane ya ce, “Shi (gwamna) ya umarci dukkanin hukumomin tsaro da su gaggauta daukan matakan ceto wadanda aka yi garkuwa da su, kuma da izinin Allah za su kubuta”.

“Mu gwamnati ne da muka san nauyin da ke kanmu kuma muna tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’ummar mu a kowani lokaci.”

Ya gargadi wadanda ke da hannu a aikace-aikacen ta’addanci da su fa sani gwamnati ba za ta taba barinsu suna cin karensu babu babbaka ba, don haka abun da ya fi musu kawai su gaggauta sauya matsayarsu su zama mutane ne kwarai.

Dukkanin wadanda suka yi magana a yayin ziyarar sun ce garkuwan da aka yi da iyalansu ya hanasu barci da sakewana kowani lokaci, sun roki gwamnati da ta yi duk mai yiyuwa wajen ceto wadanda aka yi garkuwa da su.

Gwamnatin Neja
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Gwamnatin Neja
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gwamnatin Neja
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Next Post
CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023

CDD Ga INEC: Ku Dabbaka Sahihin Zaben Da Kuka Yi A Osun, Ekiti A 2023

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Gwamnatin Neja

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gwamnatin Neja

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.