• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Sojoji A Kauyen Sudan Ya Kashe Mutum 28

byRabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Sudanese armed forces mark Army Day in Sudan's eastern Gadaref State near the border with Ethiopia on August 14, 2024. Fighting since April 15 between the forces of rival Sudanese generals vying for power has killed at least 3,900 people, according to conservative estimates by the Armed Conflict Location & Event Data Project. (Photo by AFP)

Sudanese armed forces mark Army Day in Sudan's eastern Gadaref State near the border with Ethiopia on August 14, 2024. Fighting since April 15 between the forces of rival Sudanese generals vying for power has killed at least 3,900 people, according to conservative estimates by the Armed Conflict Location & Event Data Project. (Photo by AFP)

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Dakarun sojin Sudan sun kashe akalla mutum 28 a wani hari da suka kai a wani kauye da ke Kudu da Babban Birnin Kasar Khartoum, kamar yadda kwamitin likitocin kasar ya sanar a jiya.

Kungiyar likitocin kasar Sudan ta sanar da cewa, dakarun Kai Dauki Na Musamman (RSF) sun aikata kisan kiyashi a “kauyen Um Adam” mai tazarar kilomita 150 daga Kudancin Birnin a ranar Asabar.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • Majalisar Kasa Ta Bayyana Dalilan Watsi Da Zarge-zargen Badakalar Naira Biliyan 178 A Kan Shugaban NPA

Yakin Sudan tsakanin sojoji a karkashin babban hafsan soji Abdel Fattah al-Burhan, da RSF, karkashin jagorancin tsohon mataimakinsa Mohamed Hamdan Daglo, ya fara ne a ranar 15 ga watan Afrilun da ya gabata.

An kashe dubban mutane da dama, ciki har da mutum 15,000 a wani gari guda a yankin Darfur da yaki ya daidaita, a cewar kwararru daga Majalisar Dinkin Duniya.

Yakin ya kuma raba mutane sama da miliyan 8.5 da muhallansu, tare da lalata ababen more rayuwa da Sudan ta Kudu ke fama da su, ya kuma jefa kasar cikin mawuyacin hali na yunwa.

Harin na ranar Asabar “ya yi sanadin kashe a kalla mazauna kauyuka 28 da ba su ji ba ba su gani ba, sannan fiye da mutane 240 suka jikkata”, in ji kwamitin.

Ya kara da cewa “akwai adadin wadanda suka mutu da kuma jikkatattu a kauyen wadanda ba mu iya kididdige su ba” saboda fadan da ake fama da shi da kuma wahalar isa wuraren kiwon lafiya.”

Kwamitin masu fafutuka na yankin ya bayar da adadin mutane 25 a safiyar yau.

Wata majiyar lafiya a asibitin Manakil da ke da nisan kilomita 80 ta tabbatar wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa “sun karbi masu raunuka 200, wasu daga cikinsu sun isa a makare”.

Ya kara da cewa “Muna fuskantar karancin jini kuma ba mu da isassun jami’an lafiya.”

Sama da kashi 70 cikin 100 na cibiyoyin kiwon lafiya na Sudan ba sa aiki a cewar Majalisar Dinkin Duniya, yayin da wadanda suka saura ke karbar mutane da dama fiye da karfinsu kuma suna da karancin kayan aiki.

Ana zargin bangarorin biyu da ke rikici da aikata laifukan yaki da suka hada da kai wa fararen hula hari, da yin luguden wuta ba gaira ba dalili a wuraren da jama’a ke zaune da kuma kwace da hana kayan agaji.

Tun bayan karbe ikon jihar Al-Jazira da ke Kudu da Birnin Khartoum a watan Disamba, RSF ta yi kawanya tare da kai hari ga daukacin kauyuka kamar Um Adam.

Ya zuwa watan Maris, an cinna wuta ga akalla kauyuka 108 da matsugunai a fadin kasar, abin da Cibiyar Resilience da ke Burtaniya ta gano kenan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Tirelar Sata Da Kayan Miliyan 30 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version