• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Sojoji A Kauyen Sudan Ya Kashe Mutum 28

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Harin Sojoji A Kauyen Sudan Ya Kashe Mutum 28

Sudanese armed forces mark Army Day in Sudan's eastern Gadaref State near the border with Ethiopia on August 14, 2024. Fighting since April 15 between the forces of rival Sudanese generals vying for power has killed at least 3,900 people, according to conservative estimates by the Armed Conflict Location & Event Data Project. (Photo by AFP)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

Dakarun sojin Sudan sun kashe akalla mutum 28 a wani hari da suka kai a wani kauye da ke Kudu da Babban Birnin Kasar Khartoum, kamar yadda kwamitin likitocin kasar ya sanar a jiya.

Kungiyar likitocin kasar Sudan ta sanar da cewa, dakarun Kai Dauki Na Musamman (RSF) sun aikata kisan kiyashi a “kauyen Um Adam” mai tazarar kilomita 150 daga Kudancin Birnin a ranar Asabar.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • Majalisar Kasa Ta Bayyana Dalilan Watsi Da Zarge-zargen Badakalar Naira Biliyan 178 A Kan Shugaban NPA

Yakin Sudan tsakanin sojoji a karkashin babban hafsan soji Abdel Fattah al-Burhan, da RSF, karkashin jagorancin tsohon mataimakinsa Mohamed Hamdan Daglo, ya fara ne a ranar 15 ga watan Afrilun da ya gabata.

An kashe dubban mutane da dama, ciki har da mutum 15,000 a wani gari guda a yankin Darfur da yaki ya daidaita, a cewar kwararru daga Majalisar Dinkin Duniya.

Yakin ya kuma raba mutane sama da miliyan 8.5 da muhallansu, tare da lalata ababen more rayuwa da Sudan ta Kudu ke fama da su, ya kuma jefa kasar cikin mawuyacin hali na yunwa.

Harin na ranar Asabar “ya yi sanadin kashe a kalla mazauna kauyuka 28 da ba su ji ba ba su gani ba, sannan fiye da mutane 240 suka jikkata”, in ji kwamitin.

Ya kara da cewa “akwai adadin wadanda suka mutu da kuma jikkatattu a kauyen wadanda ba mu iya kididdige su ba” saboda fadan da ake fama da shi da kuma wahalar isa wuraren kiwon lafiya.”

Kwamitin masu fafutuka na yankin ya bayar da adadin mutane 25 a safiyar yau.

Wata majiyar lafiya a asibitin Manakil da ke da nisan kilomita 80 ta tabbatar wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa “sun karbi masu raunuka 200, wasu daga cikinsu sun isa a makare”.

Ya kara da cewa “Muna fuskantar karancin jini kuma ba mu da isassun jami’an lafiya.”

Sama da kashi 70 cikin 100 na cibiyoyin kiwon lafiya na Sudan ba sa aiki a cewar Majalisar Dinkin Duniya, yayin da wadanda suka saura ke karbar mutane da dama fiye da karfinsu kuma suna da karancin kayan aiki.

Ana zargin bangarorin biyu da ke rikici da aikata laifukan yaki da suka hada da kai wa fararen hula hari, da yin luguden wuta ba gaira ba dalili a wuraren da jama’a ke zaune da kuma kwace da hana kayan agaji.

Tun bayan karbe ikon jihar Al-Jazira da ke Kudu da Birnin Khartoum a watan Disamba, RSF ta yi kawanya tare da kai hari ga daukacin kauyuka kamar Um Adam.

Ya zuwa watan Maris, an cinna wuta ga akalla kauyuka 108 da matsugunai a fadin kasar, abin da Cibiyar Resilience da ke Burtaniya ta gano kenan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Falasdinawa Na Komawa Khan Younis Yayin Da Isra’ila Ta Janye Dakarunta

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Tirelar Sata Da Kayan Miliyan 30 A Bauchi

Related

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

43 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

2 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

7 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

15 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

16 hours ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Tirelar Sata Da Kayan Miliyan 30 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.