• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Sojoji A Kauyen Sudan Ya Kashe Mutum 28

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Sudanese armed forces mark Army Day in Sudan's eastern Gadaref State near the border with Ethiopia on August 14, 2024. Fighting since April 15 between the forces of rival Sudanese generals vying for power has killed at least 3,900 people, according to conservative estimates by the Armed Conflict Location & Event Data Project. (Photo by AFP)

Sudanese armed forces mark Army Day in Sudan's eastern Gadaref State near the border with Ethiopia on August 14, 2024. Fighting since April 15 between the forces of rival Sudanese generals vying for power has killed at least 3,900 people, according to conservative estimates by the Armed Conflict Location & Event Data Project. (Photo by AFP)

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Dakarun sojin Sudan sun kashe akalla mutum 28 a wani hari da suka kai a wani kauye da ke Kudu da Babban Birnin Kasar Khartoum, kamar yadda kwamitin likitocin kasar ya sanar a jiya.

Kungiyar likitocin kasar Sudan ta sanar da cewa, dakarun Kai Dauki Na Musamman (RSF) sun aikata kisan kiyashi a “kauyen Um Adam” mai tazarar kilomita 150 daga Kudancin Birnin a ranar Asabar.

  • An Bude Baje Kolin Kayayyakin Masarufi Na Kasa Da Kasa Na Sin Karo Na 4
  • Majalisar Kasa Ta Bayyana Dalilan Watsi Da Zarge-zargen Badakalar Naira Biliyan 178 A Kan Shugaban NPA

Yakin Sudan tsakanin sojoji a karkashin babban hafsan soji Abdel Fattah al-Burhan, da RSF, karkashin jagorancin tsohon mataimakinsa Mohamed Hamdan Daglo, ya fara ne a ranar 15 ga watan Afrilun da ya gabata.

An kashe dubban mutane da dama, ciki har da mutum 15,000 a wani gari guda a yankin Darfur da yaki ya daidaita, a cewar kwararru daga Majalisar Dinkin Duniya.

Yakin ya kuma raba mutane sama da miliyan 8.5 da muhallansu, tare da lalata ababen more rayuwa da Sudan ta Kudu ke fama da su, ya kuma jefa kasar cikin mawuyacin hali na yunwa.

Harin na ranar Asabar “ya yi sanadin kashe a kalla mazauna kauyuka 28 da ba su ji ba ba su gani ba, sannan fiye da mutane 240 suka jikkata”, in ji kwamitin.

Ya kara da cewa “akwai adadin wadanda suka mutu da kuma jikkatattu a kauyen wadanda ba mu iya kididdige su ba” saboda fadan da ake fama da shi da kuma wahalar isa wuraren kiwon lafiya.”

Kwamitin masu fafutuka na yankin ya bayar da adadin mutane 25 a safiyar yau.

Wata majiyar lafiya a asibitin Manakil da ke da nisan kilomita 80 ta tabbatar wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa “sun karbi masu raunuka 200, wasu daga cikinsu sun isa a makare”.

Ya kara da cewa “Muna fuskantar karancin jini kuma ba mu da isassun jami’an lafiya.”

Sama da kashi 70 cikin 100 na cibiyoyin kiwon lafiya na Sudan ba sa aiki a cewar Majalisar Dinkin Duniya, yayin da wadanda suka saura ke karbar mutane da dama fiye da karfinsu kuma suna da karancin kayan aiki.

Ana zargin bangarorin biyu da ke rikici da aikata laifukan yaki da suka hada da kai wa fararen hula hari, da yin luguden wuta ba gaira ba dalili a wuraren da jama’a ke zaune da kuma kwace da hana kayan agaji.

Tun bayan karbe ikon jihar Al-Jazira da ke Kudu da Birnin Khartoum a watan Disamba, RSF ta yi kawanya tare da kai hari ga daukacin kauyuka kamar Um Adam.

Ya zuwa watan Maris, an cinna wuta ga akalla kauyuka 108 da matsugunai a fadin kasar, abin da Cibiyar Resilience da ke Burtaniya ta gano kenan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sudan
Labarai

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa
Labarai

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Tirelar Sata Da Kayan Miliyan 30 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sudan

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.