• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin ‘Yan Bindiga Kan Jami’an Tsaro Ya Ta Da Jijiyar Wuya A Neja

byMuhammad Awwal Umar
2 years ago
'Yan Bindiga

Sakamakon wani harin kwanton bauna da ‘yan bindiga suka yi a kan jami’an tsaro, wanda ya yi sanadin mutuwar jami’an tsaron su kimanin ashirin da biyar, wanda ya hada da jami’an soja ashirin da daya da kuma ‘yan banga hudu a Kundu da ke Karamar Hukumar Rafi, kan iyaka da Karamar Hukumar Wushishi.Hakan ya sa jama’a ke ganin akwai bukatar gwamnati ta sauya fasalin yadda aikin ke gudana a halin yanzu.

Lamarin ya faru ne a daren lahadi, inda rahotanni suka tabbatar da cewa, jami’an tsaron sun samu labarin zuwan ‘yan bindigar tafe da shanu da kuma tumakan da suka sato a kan hanyar su ta tsallakawa zuwa sansaninsu.

  • ‘Yan Bindiga Sun kashe Sojoji 23 A Neja

Jami’an tsaron sun yi kokarin yi wa ‘yan bindigar tara-tara, ba su yi aune ba sai ‘yan bindigar suka yi musu kwanton bauna; suka yi ta faman ba-ta-kashi, inda wasu rahotanni suka shaida cewa jami’an tsaron sun yi nasarar kashe sama da ‘yan bindiga hamsin, yayin da ‘yan bindigar kamar yadda rahotanni suka bayyana sun hallaka jami’an tsaron su kimanin ashirin da biyar, cikin su har da mai mukamin Kanal da Manjo da kuma ‘Yan Banga guda hudu.

A safiyar Litinin ne Gwamnan Jihar Neja, Hon. Umar Mohammed Bago ya ziyarci Shugaban Rundunar Sojan Nijeriya, inda ya bayyana masa matsalolin da jihar ke fuskanta tare da neman Rundunar ta kara kaimi a kan wanda take yi a halin yanzu da kuma ba da tabbacin gwamnatin tasa a shirye take wajen kara karfafa wa Rundunar gwiwa tare da goya mata baya don kawo karshen matsalolin tsaro a fadin jihar Neja.

Kazalika, gwamnan ya alakanta ta’azzarar matsalar tsaron da yawan fadin kasa da jihar ke da ita, domin a cewar tasa ta fi dukkanin sauran Jihohin Kasar nan yawan fadin kasa da iyakoki, kama daga Jihar Zamfara, Kebbi, Katsina da kuma Kaduna; inda mafi yawan ‘yan bindigar ke da matsugunai.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

A lokacin da gwamnan ke wannan jawabi ga Shugaban Rundunar Sojan, Janar Christopher Gwabin Musa, ya bayyana cewa jihar tasa na kewaye ne da manya-mayan rafuka da ke baiwa Sojojin matukar wahala wajen gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Kwastom Ta Kama Haramtattun Kayan Naira Biliya 1.17 Cikin Wata 8

Kwastom Ta Kama Haramtattun Kayan Naira Biliya 1.17 Cikin Wata 8

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version