ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin ‘Yan Bindiga Kan Jami’an Tsaro Ya Ta Da Jijiyar Wuya A Neja

by Muhammad Awwal Umar
3 years ago
'Yan Bindiga

Sakamakon wani harin kwanton bauna da ‘yan bindiga suka yi a kan jami’an tsaro, wanda ya yi sanadin mutuwar jami’an tsaron su kimanin ashirin da biyar, wanda ya hada da jami’an soja ashirin da daya da kuma ‘yan banga hudu a Kundu da ke Karamar Hukumar Rafi, kan iyaka da Karamar Hukumar Wushishi.Hakan ya sa jama’a ke ganin akwai bukatar gwamnati ta sauya fasalin yadda aikin ke gudana a halin yanzu.

Lamarin ya faru ne a daren lahadi, inda rahotanni suka tabbatar da cewa, jami’an tsaron sun samu labarin zuwan ‘yan bindigar tafe da shanu da kuma tumakan da suka sato a kan hanyar su ta tsallakawa zuwa sansaninsu.

  • ‘Yan Bindiga Sun kashe Sojoji 23 A Neja

Jami’an tsaron sun yi kokarin yi wa ‘yan bindigar tara-tara, ba su yi aune ba sai ‘yan bindigar suka yi musu kwanton bauna; suka yi ta faman ba-ta-kashi, inda wasu rahotanni suka shaida cewa jami’an tsaron sun yi nasarar kashe sama da ‘yan bindiga hamsin, yayin da ‘yan bindigar kamar yadda rahotanni suka bayyana sun hallaka jami’an tsaron su kimanin ashirin da biyar, cikin su har da mai mukamin Kanal da Manjo da kuma ‘Yan Banga guda hudu.

ADVERTISEMENT

A safiyar Litinin ne Gwamnan Jihar Neja, Hon. Umar Mohammed Bago ya ziyarci Shugaban Rundunar Sojan Nijeriya, inda ya bayyana masa matsalolin da jihar ke fuskanta tare da neman Rundunar ta kara kaimi a kan wanda take yi a halin yanzu da kuma ba da tabbacin gwamnatin tasa a shirye take wajen kara karfafa wa Rundunar gwiwa tare da goya mata baya don kawo karshen matsalolin tsaro a fadin jihar Neja.

Kazalika, gwamnan ya alakanta ta’azzarar matsalar tsaron da yawan fadin kasa da jihar ke da ita, domin a cewar tasa ta fi dukkanin sauran Jihohin Kasar nan yawan fadin kasa da iyakoki, kama daga Jihar Zamfara, Kebbi, Katsina da kuma Kaduna; inda mafi yawan ‘yan bindigar ke da matsugunai.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

A lokacin da gwamnan ke wannan jawabi ga Shugaban Rundunar Sojan, Janar Christopher Gwabin Musa, ya bayyana cewa jihar tasa na kewaye ne da manya-mayan rafuka da ke baiwa Sojojin matukar wahala wajen gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

'Yan Bindiga
Muhammad Awwal Umar
+ postsBio
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Kwastom Ta Kama Haramtattun Kayan Naira Biliya 1.17 Cikin Wata 8

Kwastom Ta Kama Haramtattun Kayan Naira Biliya 1.17 Cikin Wata 8

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.