• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
1 year ago
Manzon

Assalamu alaikum wa rahmtullahi ta’ala wa barkatuh. ‘Yan uwa masu karatu da ke biye da mu a wannan shafi mai albarka ina muku barka da Juma’atu babbar rana. Mako biyu da suka gabata, darasinmu yana magana ne a kan fasaha da balagar harshen Manzon Allah (SAW).

To, a wannan makon za mu dora da darasi a kan hikimomin kalaman Manzon Allah (SAW).

  • Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW) II
  • Kusantar Annabi (SAW) Da Allah

Hakika an tattaro daga kalmominsa (SAW) wanda babu wani kafin shi da ya taba fada na hikimomi a cikin duk kabilun Larabawa da wadanda ba su ba, shi ya fara fadar su. Babu wani daya daga cikin masu Hikima da za a auna shi da Annabi (SAW).

 

Yana daga cikin Hikimomin da shi ya fara fadarsu:

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Hamiyar wadisu – Tanderu sun yi zafi; Annabi (SAW) ya fada wannan a ranar yakin Hunaini, yaki ya yi yaki, Sahabbai ba dama su gudu su bar Addininsu da Annabinsu, ta bangaren Kafirai su ma sun fito da duk rayuwarsu ba dama su gudu su bar iyalansu, kowa babu damar gudu, yaki ya yi yaki, da Annabi (SAW) yaga irin yadda idon kowa ya rufe ana ta gwabza yaki sai ya ce “Hamiyar wadisu – Tanderu sun yi zafi”.

Mata Hatfa Anfihi – Ya mutu dolensa; Ma’ana ya mutu a gida ko mutuwa irin wacce take zuwa ba tare da ana tsammaninta ba, ko a ce ya mutu cikin lafiya. Larabawa a Jahiliyya da farkon Musulunci ba su so su mutu a gida, an fahimci hakan ne a fadin Sayyidina Umar ga Usman bin Maz’unu yayin da yake cewa “Ina ganin girman Usman bin Maz’unu sai da na ga ya mutu ba a wurin yaki ba, sai na ce ashe ma ba wani ba ne, har sai da na ga Annabi (SAW) Ya Mutu a gida sai na fahimci cewa mutuwar gida ba ita ke nuni da ragwanta ba”. Usman bin Maz’unu Bakuraishe ne, Sufi mai yawan Ibada, shi ne wanda da ya mutu Annabi (SAW) ya yi shaida a kabarinsa yana cewa na yi shaida ne sabida in ‘yan gidana sun mutu in bizne su kusa da shi.

La yuldagul Mumin fi Hujrin Marrataini – Ba a sarar Mumini a cikin rami daya sau biyu; Ma’ana shi Mumini mai takatsantsan ne, idan ya shiga wani lamari ya ga abin bai yi kyau ba, ba zai kara shiga ba. In kuma ya kara shiga lamarin ya sake afkuwa to ya zama wawa.

Assa’idu man wu‘iza bigairihi – Mai arziki shi ne wanda ya gargadu da abin da ya samu waninsa; Ma’ana wanda yaga wani abu ya samu dan uwansa na daga bala’i to ya kamata shi ma ya san abin da dan uwansa ya aikata hakan ta faru da shi, shi ma sai ya kiyaye kafin abin shi ma ya zo kansa.

Irin wadannan suna da yawa wanda mai karatu ba zai iya tattare su ba. Abin da mai duba zai riska su ne mamakai cikin abin da ta tattare su kuma hankali ya tattare ta na daga karshenta.

Sahabbansa sun ce da shi (Annabi Muhammad SAW) Ya Rasulullahi ba mu ga wanda ya fi ka fasaha ba, sai Annabi ya ce “Me zai hana in zama na fi kowa fasaha? Da halshena aka saukar da Alkur’ani” Ma’ana Alkur’ani yarena ne. In Bahaushe bai yi Hikima cikin Larabci ba, ba komai duk da cewa Hausawan suna shiga cikin yaren su koya har su fi ‘yan yaren kwarewa. Kusan duk masu Hadisai kyawawa guda shida ba Larabawa ba ne amma sun kware, Larabci yaren duk Musulmi ne.

Alhamdulillah, yanzu duk wannan karatun da ‘yan Nijeriya suke yi na boko, da (a ce) da yarensu ake karantarwa, da yanzu sun fara kirkire-kirkire, amma dole sai sun fara iya yaren kafin su fara neman sanin ilimin Karatun.

Sannan kuma Annabi (SAW) ya sake fada a wani lokaci “Ana afsahul Arabi, baida anni min Kuraishin, wa nasha’atu fi bani Sa’adin – Ni ne mafi fasahar Larabawa, sai dai ni dan Kuraishawa ne, kuma na tashi a cikin Bani Sa’adin” wannan nau’in maganar yana nufin karfafa yabo ta hanyar nau’in zargi.

Kamar misalin yabon wani malami ga Shehu Ibrahim Kaulaha yake cewa “Shehu Ibrahim, mutum ne mai kyauta, sai dai duk yawan abin da ya ba ka sai ya raina shi (wato shi Shehu ne zai rana abin ba wanda aka ba, ba.”

Don sabida kwadayin ‘ya’yansu su koyi fasaha, Larabawan Birni suke bawa Larabawan Kauye ‘ya’yansu su taso a kauye.

Annabi (SAW) sabida Bakuraishe ne kuma ya taso a bani Sa’adu a kauye sai aka tara masa karfin bara’uwar kauye. Yanzu mutumin kauye da ka fada masa Magana, zai dawo maka da wacce ta fi taka, har ka ji mutum yana cewa ko dai dama yana jira na ne in yi masa magana. Suna da karin magana da bakar magana.

Kuma An hada masa da gogewar lafazin birni da adon maganganun ‘yan birni sannan kuma ka hada da cewa Annabin Allah ne wanda madadinsa ke zuwa daga Allah, wanda Dan’adam bai iya kewayewa da iliminsa.

Ummu Ma’abadin ta fada cikin yadda ta siffanta Annabi (SAW) cewa Maganarsa tana da dadi, a rarrabe yake yin magana, ba magana ‘yar kadan wacce ba ta biya bukata ba kuma ba azarbabi ba (surutu, ba tsayawa, ba ma’ana), kai ka ce maganarsa tsakiya ce da aka tsara, don haka aka rubuta maganarsa a matsayin Hadisi, Manzon Allah (SAW) ya kasance mai gwarjin murya amma mai dadin murya.

Yanzu kuma bari mu juya akalar darasin namu zuwa abin da ya shafi daukakar Danganensa da girman garinsa da wajen tasowarsa mai girma (SAW).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)
Dausayin Musulunci

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi
Dausayin Musulunci

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

October 3, 2025
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.