Jami’an tsaro sun rufe hanyar shiga Majalisar Dokokin Jihar Bauchi, biyo bayan yunkurin wasu ‘yan majalisar 22 na tsige Kakakin Majalisar, Abubakar Y Sulaiman da sauran shugabannin majalisar.
Idan za a iya tunawa ‘yan majalisar dokokin Jihar 22 sun kada kuri’ar rashin kwarin guiwar kan salon jagorancin majalisar, inda suka nemi shugabanninsu da su yi murabus ko su tsigesu.
- 2023: PDP Na Bukatar Hadi Kai Don Kayar Da APC – Makarfi
- Muna Yin Siyasa Ce Bisa Tsammanin Gaba Za Ta Yi Kyau –Hajiya Halimah
Ya zuwa yanzu dai majalisar na rufe a karkashin kulawar jami’an tsaron ‘yan sanda da wasu sauran jami’an tsaro.
Hotunan yadda Majalisar ke rufe da wakilinmu ya dauka yau Litinin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp