• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hudubar Da Bakaken Fata Ke Yi Wa ‘Ya’yansu Don Tsira Daga Farmakin Fararen Amurkawa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Al'ajabi
0
Hudubar Da Bakaken Fata Ke Yi Wa ‘Ya’yansu Don Tsira Daga Farmakin Fararen Amurkawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Zan fayyace maka a matsayina na uwar ‘ya’a hudu bakaken fata: maganar ita ce tsaron kai, kan abubuwan da za ka yi ka zauna a gida lafiya.”

Reberend Najuma Smith-Pollard ta san batun sosai, wadda ta aiwatar ga danta Daniel, wanda ya mutu a 2018 yana shekara 24, kuma yanzu tana da ‘ya’ya uku ‘yan shekara 12 da 17 da kuma 18, wani lokaci kuma da ‘yarta ‘yar shekara bakwai suna zaune a Kudancin Los Angeles.

  • Masanin Ilmin Muhalli Na Zimbabwe: Hanyar Raya Kasar Sin Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ta Zama Abin Koyi Ga Duniya

Ba tattaunawa ba ce da ake yawan yi, batu ne da ake ambata lokaci daya, amma wanda ke ci gaba da wakana, da ke faruwa tsakanin iyalan bakaken fata a shekaru da dama.

“Tatattaunawa da ke ci gaba da gudana tsakanin iyaye da ‘ya’yansu game da yadda ya kamata su kare kansu a rayuwa ta yau da kullum,” in ji Smith-Pollard wadda take bayyana kwarewarta a matsayinta na malamar kirista kuma shugabar al’umma a wurin aikinta na Cibiyar Nazarin Harakokin Addini da Al’adu a Jami’ar Southern California (USC).

“A matsayina na uwar ‘ya’ya bakaken fata da ke zama a birni, ina magana da su game da ‘yan sanda da kuma masu laifi, domin akwai mutane makwabta wadanda ba su da mugunyar aniya.
“Ina koya masu yadda za su yi mu’amula da jami’an tsaro da kuma rayuwa gaba daya, a cewarta.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

Wanda aka fi sani da “The Talk, shi ne da’awar yau da kullum na abin da masana ilimi ke kira launin fata da zamantakewar kabilanci, wanda fage ne na nazari a fannin ilimin zamantakewa da halayyar Dan‘adam.

Akwai dimbin rubuce-rubucen kimiyya game da maudu’in da shirye-shirye kamar ‘The Talk’: ‘Race in America’ da ake gabatarwa a kafar talabijin na PBS a Amurka.

Da yawa akwai wadanda suka yi magana da yan jaridu sannan kuma kwai wadanda suka ki amincewa, amma dai sun bayyana shirin “The Talk” a matsayin wani abu mai daci, wani nauyi da iyalan Amurkawa ‘yan asalin Afirka da Latino suke hakuri da shi.

“Yanzu da ake yawan samun rikicin wariyar launin fata, haka kuma dole mu fara fadar matasarmu cewa, kada ku taba yarda da fararen fata ‘yan shekara 18,” in ji Smith-Pollard.

Tana ba da misali da harin bindiga a ranar 14 ga Mayu da mutum 10 suka mutu a wani babban kanti a Bufallo, New York inda bakaken fata suka fi yawa.

‘Yansanda
“Ta tattauna tsakaninta da babban danta ne lokacin da ya kai shekara 13. Yana aji bakwai wasu suka kai masa hari a kan hanyarsa ta zuwa dakin karatu tare da abokin karatunsa.

“Dole na fada maka, a duk lokacin da kai da abokinka kuka fita, ka dinga kula da wanda kake tare da su.”
Wannan sakon game matakan tsaronsa ana maimaita masa a duk lokacin da zai fita shi kadai, amma abin ya sauya bayan ya samu lasisin tuki.

“Lokacin da ya fara tuki dole na fara magana da shi game da abin da ya dace ya yi da kuma abin da bai dace ba, idan har ka yi karo da ‘yan sanda,” in ji ta.
Tattaunawar ta fara ne kamar haka, kamar yadda take tunawa: “Mun zauna a Los Angeles, bangaren Kudanci.

Ba sai ka yi wani abu marar kyau ba kafin a kama ka. Za su iya cewa ka tsaya, su tuhume ka. Ya kamata ka san cewa kana da ‘yanci.” In ji ta.
Ta riga ta fada masa game da ‘yancinsa lokacin da ya cika shekara 15, saboda kamanninsa – shi dogo ne kuma kakkaura, ya buga wasan a kwallo Amurka tun yana shekara tara kuma yawanci mutane na daukarsa mai yawan shekaru.

“Kada ka bari wani ya fara bincikenka ba tare da yana da sammaci ba. Ba dole sai ka amsa tambayoyi ba, domin kai yaro ne. Za ka iya kiran mahaifiyarka, ka sa su kira ni nan-take.

“Kada ka damu idan har suna son tafiya da kai ofishin ‘yan sanda, kada ka yi fada kuma kada ka gudu. Mahaifinka da ni za mu yi kokarin fitar da kai daga ko wace irin fitina.”

“Ka fada masu sunanka kuma ka nuna masu katinka na shaida. Abubuwan da za ka ba su kenan, kuma ya fi dacewa su duba da kansu domin tabbatar da ba ka taba aikata laifi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sirrukan Mata Da Maza Ba Su Sani Ba (3): Mace Tana Da Tausayi, Sai Dai Akwai Gorantawa

Next Post

Hanyoyin Amfani Da Telegram

Related

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

1 week ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

1 week ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

3 weeks ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

2 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

3 months ago
Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja
Al'ajabi

Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja

4 months ago
Next Post
Hanyoyin Amfani Da Telegram

Hanyoyin Amfani Da Telegram

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.