• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hudubar Da Bakaken Fata Ke Yi Wa ‘Ya’yansu Don Tsira Daga Farmakin Fararen Amurkawa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Bakaken fata

“Zan fayyace maka a matsayina na uwar ‘ya’a hudu bakaken fata: maganar ita ce tsaron kai, kan abubuwan da za ka yi ka zauna a gida lafiya.”

Reberend Najuma Smith-Pollard ta san batun sosai, wadda ta aiwatar ga danta Daniel, wanda ya mutu a 2018 yana shekara 24, kuma yanzu tana da ‘ya’ya uku ‘yan shekara 12 da 17 da kuma 18, wani lokaci kuma da ‘yarta ‘yar shekara bakwai suna zaune a Kudancin Los Angeles.

  • Masanin Ilmin Muhalli Na Zimbabwe: Hanyar Raya Kasar Sin Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ta Zama Abin Koyi Ga Duniya

Ba tattaunawa ba ce da ake yawan yi, batu ne da ake ambata lokaci daya, amma wanda ke ci gaba da wakana, da ke faruwa tsakanin iyalan bakaken fata a shekaru da dama.

“Tatattaunawa da ke ci gaba da gudana tsakanin iyaye da ‘ya’yansu game da yadda ya kamata su kare kansu a rayuwa ta yau da kullum,” in ji Smith-Pollard wadda take bayyana kwarewarta a matsayinta na malamar kirista kuma shugabar al’umma a wurin aikinta na Cibiyar Nazarin Harakokin Addini da Al’adu a Jami’ar Southern California (USC).

“A matsayina na uwar ‘ya’ya bakaken fata da ke zama a birni, ina magana da su game da ‘yan sanda da kuma masu laifi, domin akwai mutane makwabta wadanda ba su da mugunyar aniya.
“Ina koya masu yadda za su yi mu’amula da jami’an tsaro da kuma rayuwa gaba daya, a cewarta.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Wanda aka fi sani da “The Talk, shi ne da’awar yau da kullum na abin da masana ilimi ke kira launin fata da zamantakewar kabilanci, wanda fage ne na nazari a fannin ilimin zamantakewa da halayyar Dan‘adam.

Akwai dimbin rubuce-rubucen kimiyya game da maudu’in da shirye-shirye kamar ‘The Talk’: ‘Race in America’ da ake gabatarwa a kafar talabijin na PBS a Amurka.

Da yawa akwai wadanda suka yi magana da yan jaridu sannan kuma kwai wadanda suka ki amincewa, amma dai sun bayyana shirin “The Talk” a matsayin wani abu mai daci, wani nauyi da iyalan Amurkawa ‘yan asalin Afirka da Latino suke hakuri da shi.

“Yanzu da ake yawan samun rikicin wariyar launin fata, haka kuma dole mu fara fadar matasarmu cewa, kada ku taba yarda da fararen fata ‘yan shekara 18,” in ji Smith-Pollard.

Tana ba da misali da harin bindiga a ranar 14 ga Mayu da mutum 10 suka mutu a wani babban kanti a Bufallo, New York inda bakaken fata suka fi yawa.

‘Yansanda
“Ta tattauna tsakaninta da babban danta ne lokacin da ya kai shekara 13. Yana aji bakwai wasu suka kai masa hari a kan hanyarsa ta zuwa dakin karatu tare da abokin karatunsa.

“Dole na fada maka, a duk lokacin da kai da abokinka kuka fita, ka dinga kula da wanda kake tare da su.”
Wannan sakon game matakan tsaronsa ana maimaita masa a duk lokacin da zai fita shi kadai, amma abin ya sauya bayan ya samu lasisin tuki.

“Lokacin da ya fara tuki dole na fara magana da shi game da abin da ya dace ya yi da kuma abin da bai dace ba, idan har ka yi karo da ‘yan sanda,” in ji ta.
Tattaunawar ta fara ne kamar haka, kamar yadda take tunawa: “Mun zauna a Los Angeles, bangaren Kudanci.

Ba sai ka yi wani abu marar kyau ba kafin a kama ka. Za su iya cewa ka tsaya, su tuhume ka. Ya kamata ka san cewa kana da ‘yanci.” In ji ta.
Ta riga ta fada masa game da ‘yancinsa lokacin da ya cika shekara 15, saboda kamanninsa – shi dogo ne kuma kakkaura, ya buga wasan a kwallo Amurka tun yana shekara tara kuma yawanci mutane na daukarsa mai yawan shekaru.

“Kada ka bari wani ya fara bincikenka ba tare da yana da sammaci ba. Ba dole sai ka amsa tambayoyi ba, domin kai yaro ne. Za ka iya kiran mahaifiyarka, ka sa su kira ni nan-take.

“Kada ka damu idan har suna son tafiya da kai ofishin ‘yan sanda, kada ka yi fada kuma kada ka gudu. Mahaifinka da ni za mu yi kokarin fitar da kai daga ko wace irin fitina.”

“Ka fada masu sunanka kuma ka nuna masu katinka na shaida. Abubuwan da za ka ba su kenan, kuma ya fi dacewa su duba da kansu domin tabbatar da ba ka taba aikata laifi ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Next Post
Hanyoyin Amfani Da Telegram

Hanyoyin Amfani Da Telegram

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.