ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hudubar Da Bakaken Fata Ke Yi Wa ‘Ya’yansu Don Tsira Daga Farmakin Fararen Amurkawa

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Bakaken fata

“Zan fayyace maka a matsayina na uwar ‘ya’a hudu bakaken fata: maganar ita ce tsaron kai, kan abubuwan da za ka yi ka zauna a gida lafiya.”

Reberend Najuma Smith-Pollard ta san batun sosai, wadda ta aiwatar ga danta Daniel, wanda ya mutu a 2018 yana shekara 24, kuma yanzu tana da ‘ya’ya uku ‘yan shekara 12 da 17 da kuma 18, wani lokaci kuma da ‘yarta ‘yar shekara bakwai suna zaune a Kudancin Los Angeles.

  • Masanin Ilmin Muhalli Na Zimbabwe: Hanyar Raya Kasar Sin Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba Ta Zama Abin Koyi Ga Duniya

Ba tattaunawa ba ce da ake yawan yi, batu ne da ake ambata lokaci daya, amma wanda ke ci gaba da wakana, da ke faruwa tsakanin iyalan bakaken fata a shekaru da dama.

ADVERTISEMENT

“Tatattaunawa da ke ci gaba da gudana tsakanin iyaye da ‘ya’yansu game da yadda ya kamata su kare kansu a rayuwa ta yau da kullum,” in ji Smith-Pollard wadda take bayyana kwarewarta a matsayinta na malamar kirista kuma shugabar al’umma a wurin aikinta na Cibiyar Nazarin Harakokin Addini da Al’adu a Jami’ar Southern California (USC).

“A matsayina na uwar ‘ya’ya bakaken fata da ke zama a birni, ina magana da su game da ‘yan sanda da kuma masu laifi, domin akwai mutane makwabta wadanda ba su da mugunyar aniya.
“Ina koya masu yadda za su yi mu’amula da jami’an tsaro da kuma rayuwa gaba daya, a cewarta.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Wanda aka fi sani da “The Talk, shi ne da’awar yau da kullum na abin da masana ilimi ke kira launin fata da zamantakewar kabilanci, wanda fage ne na nazari a fannin ilimin zamantakewa da halayyar Dan‘adam.

Akwai dimbin rubuce-rubucen kimiyya game da maudu’in da shirye-shirye kamar ‘The Talk’: ‘Race in America’ da ake gabatarwa a kafar talabijin na PBS a Amurka.

Da yawa akwai wadanda suka yi magana da yan jaridu sannan kuma kwai wadanda suka ki amincewa, amma dai sun bayyana shirin “The Talk” a matsayin wani abu mai daci, wani nauyi da iyalan Amurkawa ‘yan asalin Afirka da Latino suke hakuri da shi.

“Yanzu da ake yawan samun rikicin wariyar launin fata, haka kuma dole mu fara fadar matasarmu cewa, kada ku taba yarda da fararen fata ‘yan shekara 18,” in ji Smith-Pollard.

Tana ba da misali da harin bindiga a ranar 14 ga Mayu da mutum 10 suka mutu a wani babban kanti a Bufallo, New York inda bakaken fata suka fi yawa.

‘Yansanda
“Ta tattauna tsakaninta da babban danta ne lokacin da ya kai shekara 13. Yana aji bakwai wasu suka kai masa hari a kan hanyarsa ta zuwa dakin karatu tare da abokin karatunsa.

“Dole na fada maka, a duk lokacin da kai da abokinka kuka fita, ka dinga kula da wanda kake tare da su.”
Wannan sakon game matakan tsaronsa ana maimaita masa a duk lokacin da zai fita shi kadai, amma abin ya sauya bayan ya samu lasisin tuki.

“Lokacin da ya fara tuki dole na fara magana da shi game da abin da ya dace ya yi da kuma abin da bai dace ba, idan har ka yi karo da ‘yan sanda,” in ji ta.
Tattaunawar ta fara ne kamar haka, kamar yadda take tunawa: “Mun zauna a Los Angeles, bangaren Kudanci.

Ba sai ka yi wani abu marar kyau ba kafin a kama ka. Za su iya cewa ka tsaya, su tuhume ka. Ya kamata ka san cewa kana da ‘yanci.” In ji ta.
Ta riga ta fada masa game da ‘yancinsa lokacin da ya cika shekara 15, saboda kamanninsa – shi dogo ne kuma kakkaura, ya buga wasan a kwallo Amurka tun yana shekara tara kuma yawanci mutane na daukarsa mai yawan shekaru.

“Kada ka bari wani ya fara bincikenka ba tare da yana da sammaci ba. Ba dole sai ka amsa tambayoyi ba, domin kai yaro ne. Za ka iya kiran mahaifiyarka, ka sa su kira ni nan-take.

“Kada ka damu idan har suna son tafiya da kai ofishin ‘yan sanda, kada ka yi fada kuma kada ka gudu. Mahaifinka da ni za mu yi kokarin fitar da kai daga ko wace irin fitina.”

“Ka fada masu sunanka kuma ka nuna masu katinka na shaida. Abubuwan da za ka ba su kenan, kuma ya fi dacewa su duba da kansu domin tabbatar da ba ka taba aikata laifi ba.

Bakaken fata
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
Next Post
Hanyoyin Amfani Da Telegram

Hanyoyin Amfani Da Telegram

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.