• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai, Makala
0
Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kare hakkin Bil’adama ta kasa (NHRC) ta ce ta amshi koke san cin zaraf-in take hakkin Bil’adama har guda 55,218 a watan Mayu da tattaro a jihohin da suke fadin Nijeriya, manyan korafe-korafe an samesu ne a kan masu madafun iko da suke jihohi daban-daban.

Sakataren hukumar, Dakta Anthony Ojukwu shi ne ya shaida hakan a makon jiya, yayin da ke gabatar da bayani kan yawan kesa-kesan cin zarafin mutane da aka samu a watan Mayu da ya gudana a Abuja. Ya nuna takaicinsa kan cewa kaso mafi tsoka na kauye hakkin an samesu ne kan masu madafin iko.

  • Me Yake Faruwa Da Kungiyar Brighton A Kakar Bana?
  • Haaland Ba Zai Samu Buga Wasan Man City Da Brighton Ba A Yau Alhamis

Ya kuma nuna damuwa kan cewa masu rike da madafun iko da ya dace a ce suke tabbatar da yin duk mai yiyuwa domin ganin an kare hakkin al’umma, ba wai su kasance ja gaba wajen tauye musu hakkinsu ba.

Ojukwu ya nuna cewa akwai bukatar gwamnatocin jihohi da na tarayya da su dauki kwararan matakan shawo kan cin zarafin mutane ta hanyar aiwatar da shirye-shiryen da za su inganta samar da ilimi ga kowa, kiwon lafiya, gidaje, da kuma samar da damarmakin ayyukan yi.

Ya ce hakan zai taimaka wajen kare hakkin jama’a da kuma ba su damar morar tattalin arzikinsu, jin dadi da walwa hadi da hakkin al’adu ba tare da nuna bam-bance-bambance ko tsangwama ba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Da yake nuna takaici kan yadda kashe-kashe da garkuwa da mutane ke ci gaba da karuwa, babban Lauyan Nijeriya (SAN) ya yi tambayar kan yadda ake samun karuwar kamewa da tsare ‘yan jarida a kasar nan, kari kan yawan kashe jami’an tsaro, karuwar cin zarafin yara kanana gami da tasirin sauye-sauyen tattalin arziki wanda a cewarsa hakan na kara rage wa jama’a jin dadin hakkinsu a fadin kasar nan.

Shugaban NHRC ya kuma nuna takaicin hukumar na cewa a watan Mayu, sun shaidi korafe-korafen keta wa yara kanana haddi tare da cewa sama da kesa-kesai 31,288 da 7,560 an shigar da su ne kan masu madafun iko da wadanda ba su rike da madafun iko a cikin wannan wa’adin.

Ya ce, wannan adadin na tauye hakkin jama’a na zuwa ne dukd a kokarin da hukumar ke yi na dakile hakan. Ya ce, dole ne a nanata muhimmanci da ke akwai wajen bin matakan da suka dace domin wanzar da gaskiya, da kuma tabbatar da cewa jami’an tsaro na bin matakan da suka dace daidai da yadda doka ya tanadar musu.

A cewarsa, hukumar ta kuma samu rahoton kashe-kashe 298 da garkuwa da mu-tane 360 a cikin watan na Mayu da ‘yan bindiga dadi suka aikata.

Ya bukaci gwamnati da ta tashi tsaye wajen magance matsalar tauye hakkin jama’a da kuma tabbatar da cewa jama’a na cin gajiyar tattalin arzikinsu, walwala da jin dadi da kuma al’adu ba tare da nuna bambanci ko tsangwama ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HukumaHuman rights
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

Next Post

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

Related

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

19 minutes ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

1 hour ago
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 
Labarai

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

2 hours ago
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 
Labarai

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

3 hours ago
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja
Manyan Labarai

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

4 hours ago
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
Labarai

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

5 hours ago
Next Post
Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

August 10, 2025
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.