ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Hukuma

Hukumar kare hakkin Bil’adama ta kasa (NHRC) ta ce ta amshi koke san cin zaraf-in take hakkin Bil’adama har guda 55,218 a watan Mayu da tattaro a jihohin da suke fadin Nijeriya, manyan korafe-korafe an samesu ne a kan masu madafun iko da suke jihohi daban-daban.

Sakataren hukumar, Dakta Anthony Ojukwu shi ne ya shaida hakan a makon jiya, yayin da ke gabatar da bayani kan yawan kesa-kesan cin zarafin mutane da aka samu a watan Mayu da ya gudana a Abuja. Ya nuna takaicinsa kan cewa kaso mafi tsoka na kauye hakkin an samesu ne kan masu madafin iko.

  • Me Yake Faruwa Da Kungiyar Brighton A Kakar Bana?
  • Haaland Ba Zai Samu Buga Wasan Man City Da Brighton Ba A Yau Alhamis

Ya kuma nuna damuwa kan cewa masu rike da madafun iko da ya dace a ce suke tabbatar da yin duk mai yiyuwa domin ganin an kare hakkin al’umma, ba wai su kasance ja gaba wajen tauye musu hakkinsu ba.

ADVERTISEMENT

Ojukwu ya nuna cewa akwai bukatar gwamnatocin jihohi da na tarayya da su dauki kwararan matakan shawo kan cin zarafin mutane ta hanyar aiwatar da shirye-shiryen da za su inganta samar da ilimi ga kowa, kiwon lafiya, gidaje, da kuma samar da damarmakin ayyukan yi.

Ya ce hakan zai taimaka wajen kare hakkin jama’a da kuma ba su damar morar tattalin arzikinsu, jin dadi da walwa hadi da hakkin al’adu ba tare da nuna bam-bance-bambance ko tsangwama ba.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Da yake nuna takaici kan yadda kashe-kashe da garkuwa da mutane ke ci gaba da karuwa, babban Lauyan Nijeriya (SAN) ya yi tambayar kan yadda ake samun karuwar kamewa da tsare ‘yan jarida a kasar nan, kari kan yawan kashe jami’an tsaro, karuwar cin zarafin yara kanana gami da tasirin sauye-sauyen tattalin arziki wanda a cewarsa hakan na kara rage wa jama’a jin dadin hakkinsu a fadin kasar nan.

Shugaban NHRC ya kuma nuna takaicin hukumar na cewa a watan Mayu, sun shaidi korafe-korafen keta wa yara kanana haddi tare da cewa sama da kesa-kesai 31,288 da 7,560 an shigar da su ne kan masu madafun iko da wadanda ba su rike da madafun iko a cikin wannan wa’adin.

Ya ce, wannan adadin na tauye hakkin jama’a na zuwa ne dukd a kokarin da hukumar ke yi na dakile hakan. Ya ce, dole ne a nanata muhimmanci da ke akwai wajen bin matakan da suka dace domin wanzar da gaskiya, da kuma tabbatar da cewa jami’an tsaro na bin matakan da suka dace daidai da yadda doka ya tanadar musu.

A cewarsa, hukumar ta kuma samu rahoton kashe-kashe 298 da garkuwa da mu-tane 360 a cikin watan na Mayu da ‘yan bindiga dadi suka aikata.

Ya bukaci gwamnati da ta tashi tsaye wajen magance matsalar tauye hakkin jama’a da kuma tabbatar da cewa jama’a na cin gajiyar tattalin arzikinsu, walwala da jin dadi da kuma al’adu ba tare da nuna bambanci ko tsangwama ba.

Hukuma
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.