ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Hukuma

Hukumar kare hakkin Bil’adama ta kasa (NHRC) ta ce ta amshi koke san cin zaraf-in take hakkin Bil’adama har guda 55,218 a watan Mayu da tattaro a jihohin da suke fadin Nijeriya, manyan korafe-korafe an samesu ne a kan masu madafun iko da suke jihohi daban-daban.

Sakataren hukumar, Dakta Anthony Ojukwu shi ne ya shaida hakan a makon jiya, yayin da ke gabatar da bayani kan yawan kesa-kesan cin zarafin mutane da aka samu a watan Mayu da ya gudana a Abuja. Ya nuna takaicinsa kan cewa kaso mafi tsoka na kauye hakkin an samesu ne kan masu madafin iko.

  • Me Yake Faruwa Da Kungiyar Brighton A Kakar Bana?
  • Haaland Ba Zai Samu Buga Wasan Man City Da Brighton Ba A Yau Alhamis

Ya kuma nuna damuwa kan cewa masu rike da madafun iko da ya dace a ce suke tabbatar da yin duk mai yiyuwa domin ganin an kare hakkin al’umma, ba wai su kasance ja gaba wajen tauye musu hakkinsu ba.

ADVERTISEMENT

Ojukwu ya nuna cewa akwai bukatar gwamnatocin jihohi da na tarayya da su dauki kwararan matakan shawo kan cin zarafin mutane ta hanyar aiwatar da shirye-shiryen da za su inganta samar da ilimi ga kowa, kiwon lafiya, gidaje, da kuma samar da damarmakin ayyukan yi.

Ya ce hakan zai taimaka wajen kare hakkin jama’a da kuma ba su damar morar tattalin arzikinsu, jin dadi da walwa hadi da hakkin al’adu ba tare da nuna bam-bance-bambance ko tsangwama ba.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Da yake nuna takaici kan yadda kashe-kashe da garkuwa da mutane ke ci gaba da karuwa, babban Lauyan Nijeriya (SAN) ya yi tambayar kan yadda ake samun karuwar kamewa da tsare ‘yan jarida a kasar nan, kari kan yawan kashe jami’an tsaro, karuwar cin zarafin yara kanana gami da tasirin sauye-sauyen tattalin arziki wanda a cewarsa hakan na kara rage wa jama’a jin dadin hakkinsu a fadin kasar nan.

Shugaban NHRC ya kuma nuna takaicin hukumar na cewa a watan Mayu, sun shaidi korafe-korafen keta wa yara kanana haddi tare da cewa sama da kesa-kesai 31,288 da 7,560 an shigar da su ne kan masu madafun iko da wadanda ba su rike da madafun iko a cikin wannan wa’adin.

Ya ce, wannan adadin na tauye hakkin jama’a na zuwa ne dukd a kokarin da hukumar ke yi na dakile hakan. Ya ce, dole ne a nanata muhimmanci da ke akwai wajen bin matakan da suka dace domin wanzar da gaskiya, da kuma tabbatar da cewa jami’an tsaro na bin matakan da suka dace daidai da yadda doka ya tanadar musu.

A cewarsa, hukumar ta kuma samu rahoton kashe-kashe 298 da garkuwa da mu-tane 360 a cikin watan na Mayu da ‘yan bindiga dadi suka aikata.

Ya bukaci gwamnati da ta tashi tsaye wajen magance matsalar tauye hakkin jama’a da kuma tabbatar da cewa jama’a na cin gajiyar tattalin arzikinsu, walwala da jin dadi da kuma al’adu ba tare da nuna bambanci ko tsangwama ba.

Hukuma
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Litinin Da Talata A Matsayin Ranakun Hutu

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.