ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Alhazai Ta Jihar Kebbi Ta Samu Sabon Shugaba

by Abdullahi Faruk
3 years ago
Kebbi

Sabon Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kebbi, Alhaji Faruk Musa Yaro Enabo, ya bai wa Gwamna Nasir Idris da al’ummar Jihar tabbacin gudanar da aikin Hajji nagari.

Shugaban ya nuna matukar godiya ga Gwamna Idris bisa samun sa da ya cancanci a nada shi a irin wannan matsayi mai girma, inda ya yi alkawarin sauke dimbin amanar da aka dora masa.

  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi
  • Ku Yi Aiki Tukuru Ko Na Kore Ku, Tinubu Ga Ministoci

Shugaban hukumar ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar ragamar jagorancin hukumar a Birnin Kebbi, da kuma yin jawabi ga ma’aikatan hukumar da masu fatan alheri.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya gode wa Allah da ya ba shi wannan aiki na addini mai daraja, sannan ya sanya fata da amana, shi domin shiriya da taimako don sauke nauyin da ke kansa da matukar nasara.

Alhaji Faruk Musa ya bayyana sauran mambobin hukumar a matsayin fitattun mutane, inda ya ba da tabbacin cewa za su fara aiki nan take domin samun kyakkyawan aikin Hajji na aikin hajji mai zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Haka kuma ya yi bayanin tsarin bizar da kasar Saudiyya ta yi na aikin Hajjin shekarar 2024, inda ya bayyana cewa, sabanin abin da aka samu a baya na wahalar da ake fuskanta na ba da biza cikin kankanin lokaci, bayar da bizar ga maniyyata daga yanzu zai dogara ne kan biyan kudin aikin Hajji gaba daya.

Sai dai ya bayyana cewa da zarar duk wani mahajjaci ya biya kudinsa gaba daya, hukumomin kasar Saudiyya za su ba shi bizar, inda ya ce tuni aka bude hanyar shiga ta kuma za a rufe bayan mako uku.

Shugaban ya sanar da duk mai niyyar zuwa aikin Hajji cewa makonni biyu kacal a cikinsu su biya kudin aikin Hajjin da ya kai Naira miliyan 4.5 sannan ya bukace su da su gaggauta biya.

Tun da farko, a jawabin maraba Alhaji Sani Idris Abarshi, sakataren hukumar ya bayyana farin cikinsa da nadin Faruq Musa Yaro Enabo a matsayin shugabanta, inda ya bayyana shi a matsayin wanda ya kware da kwazo.

Alhaji Sani Abarshi, ya yaba wa Gwamna Nasir Idris bisa amincewa da Alhaji Faruk Musa wajen tafiyar da harkokin Hukumar Jin Dadin Alhazai, inda ya yi alkawarin ba shi dukkan goyon baya da hadin kai don samun nasara.

Cikin wadanda suka raka shugaban domin karbar ragamar mulki har da shugaban jam’iyyar APC na jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Muhammad Kana Zuru da dimbin masoya da abokan arziki.

Kebbi
Abdullahi Faruk
+ postsBio

    MASU ALAKA

    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
    Labarai

    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

    July 14, 2026
    Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
    Manyan Labarai

    Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

    July 14, 2026
    Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
    Labarai

    Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

    July 14, 2026
    Next Post
    Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

    Kotu Ta Dakatar Da Majalisar Dokokin Ribas Daga Tsige Fubara

    LABARAI MASU NASABA

    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

    July 14, 2026
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

    July 14, 2026
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

    July 14, 2026
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

    July 14, 2026
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

    July 14, 2026
    Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

    Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

    July 14, 2026
    An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

    An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

    July 14, 2026
    Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

    Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

    July 14, 2026
    Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

    Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

    July 14, 2026
    CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

    CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

    July 14, 2026

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

    No Result
    View All Result
    • Gida
    • Labarai
      • Manyan Labarai
      • Kananan Labarai
      • Masarautu
      • Bakon Marubuci
      • Dausayin Musulunci
      • Daga Kasar Sin
      • Nishadi
      • Noma Da Kiwo
      • Sana’a Sa’a
      • Tambarin Dimokuradiyya
      • Taskira
      • Daga Birnin Sin
      • Ado Da Kwalliya
    • Siyasa
    • Wasanni
    • Al’adu
    • Al’ajabi
    • Labaran Kasuwanci
    • Karanta cikin Turanci

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.