• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Kaduna Ta Fara Horas Da Malamai 8,500 Fasahar Kwamfuta A Fadin Jihar

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Kaduna Ta Fara Horas Da Malamai 8,500 Fasahar Kwamfuta A Fadin Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Jihar Kaduna, SUBEB ta kaddamar da horas da Malaman firamare 8,500 fasahar amfani da kwamfuta don inganta harkar karantarwa a fadin kananan hukumomi 23 da ke jihar.

Babbar Mamba a ofishin jin dadin ma’aikara ta SUBEB, Dr Christy Ayi Aladimerin ta taya Malaman murna da kasancewarsu daga cikin wadanda za su samu horon, inda ta ce, tana fatan za su yi amfani da Ilimin da suka samu ba don amfanin kashin kansu kadai ba har zuwa ga dalibansu.

  • Manoman Rani Za Su Samu Tallafin Noma Na Gwamnatin Tarayya Da Kashi 50 Cikin 100
  • Kowacce Yarinya Za Ta Samu Ilimi Da Sana’a A Jihar Katsina – Gwamnati

Ta kara da cewa, horaswar tana gudana ne a shiyyoyi Uku da ke fadin jihar – Zariya, Tsakiyar Kaduna da Kafanchan, kuma an zakulo Malaman ne daga duk Kananan hukumomin 23 da ke fadin jihar. Za a yi mako guda ana horas da Malaman inda aka fara daga yau Litinin 11 ga Watan Disamba,  2023.

A nasa jawabin, yayin da yake kaddamar da horas da Malaman, Babban Sakataren zartaswa na SUBEB, Alhaji Tijjani Abdullahi, ya ce, domin cika alkawurran da suka dauka na inganta bangaren ilimi, yasa suka shirya wannan horaswar a karkashin shirin (BESDA) ta yadda Malaman za su iya amfani da kwamfuta wajen bincike da kwarewa don amfanar dalibansu.

Hukumar Ilimi
Wasu daga cikin Malaman da suke amsa horo a dakin Kwamfuta na Jami’ar jihar Kadua.

Alhaji Tijjani ya bayyana amfanin sanin ilimin kwamfuta a wannan zamani da cewa, ya zama dole musamman a bangaren karantarwa. Ya kuma ja hankalin Malaman da su ci gaba da neman ilimin kwamfuta domin kara inganta karantarwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

“Babban burin da muke son cimmawa a wannan horaswar da muka shiryawa Malamanmu shi ne, mu horas da su amfani da kwamfuta don karantar da dalibai, ta yadda za su iya bincike da neman kayan karatu a intanet.

Hukumar Ilimi
Dr Christy Ayi Aladimerin Permanent Member Human Resources, yayin da take jawabi ga mahalarta taron a dakin Kwamfuta da ke jami’ar KASU

“Da yawan Malaman da muke da su, za ka lura cewa, kamar suna tsoron taba kwamfuta, duk da cewa suna amfani da manyan salular zamani (Android). Don haka, muna fata Malaman, za su samu horo sosai a fannin amfani da kwamfuta don binciken sabbin kayan karantarwa.” Inji Tijjani

Daga karshe, Babban Sakataren, ya jaddada cewa, za su dunga gudanar da bincike a makarantu domin tabbatar da ganin Malaman suna amfanar Dalibai da Ilimin da suka samu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SubebUBEC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Sake Mika Ta’aziyyarsa Ga Iyalan Da Harin Bam Ya Rutsa A Tudun Biri, Kaduna 

Next Post

Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

3 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

10 hours ago
Next Post
Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.