• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Kaduna Ta Fara Horas Da Malamai 8,500 Fasahar Kwamfuta A Fadin Jihar

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Kaduna Ta Fara Horas Da Malamai 8,500 Fasahar Kwamfuta A Fadin Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Jihar Kaduna, SUBEB ta kaddamar da horas da Malaman firamare 8,500 fasahar amfani da kwamfuta don inganta harkar karantarwa a fadin kananan hukumomi 23 da ke jihar.

Babbar Mamba a ofishin jin dadin ma’aikara ta SUBEB, Dr Christy Ayi Aladimerin ta taya Malaman murna da kasancewarsu daga cikin wadanda za su samu horon, inda ta ce, tana fatan za su yi amfani da Ilimin da suka samu ba don amfanin kashin kansu kadai ba har zuwa ga dalibansu.

  • Manoman Rani Za Su Samu Tallafin Noma Na Gwamnatin Tarayya Da Kashi 50 Cikin 100
  • Kowacce Yarinya Za Ta Samu Ilimi Da Sana’a A Jihar Katsina – Gwamnati

Ta kara da cewa, horaswar tana gudana ne a shiyyoyi Uku da ke fadin jihar – Zariya, Tsakiyar Kaduna da Kafanchan, kuma an zakulo Malaman ne daga duk Kananan hukumomin 23 da ke fadin jihar. Za a yi mako guda ana horas da Malaman inda aka fara daga yau Litinin 11 ga Watan Disamba,  2023.

A nasa jawabin, yayin da yake kaddamar da horas da Malaman, Babban Sakataren zartaswa na SUBEB, Alhaji Tijjani Abdullahi, ya ce, domin cika alkawurran da suka dauka na inganta bangaren ilimi, yasa suka shirya wannan horaswar a karkashin shirin (BESDA) ta yadda Malaman za su iya amfani da kwamfuta wajen bincike da kwarewa don amfanar dalibansu.

Hukumar Ilimi
Wasu daga cikin Malaman da suke amsa horo a dakin Kwamfuta na Jami’ar jihar Kadua.

Alhaji Tijjani ya bayyana amfanin sanin ilimin kwamfuta a wannan zamani da cewa, ya zama dole musamman a bangaren karantarwa. Ya kuma ja hankalin Malaman da su ci gaba da neman ilimin kwamfuta domin kara inganta karantarwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

“Babban burin da muke son cimmawa a wannan horaswar da muka shiryawa Malamanmu shi ne, mu horas da su amfani da kwamfuta don karantar da dalibai, ta yadda za su iya bincike da neman kayan karatu a intanet.

Hukumar Ilimi
Dr Christy Ayi Aladimerin Permanent Member Human Resources, yayin da take jawabi ga mahalarta taron a dakin Kwamfuta da ke jami’ar KASU

“Da yawan Malaman da muke da su, za ka lura cewa, kamar suna tsoron taba kwamfuta, duk da cewa suna amfani da manyan salular zamani (Android). Don haka, muna fata Malaman, za su samu horo sosai a fannin amfani da kwamfuta don binciken sabbin kayan karantarwa.” Inji Tijjani

Daga karshe, Babban Sakataren, ya jaddada cewa, za su dunga gudanar da bincike a makarantu domin tabbatar da ganin Malaman suna amfanar Dalibai da Ilimin da suka samu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SubebUBEC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Sake Mika Ta’aziyyarsa Ga Iyalan Da Harin Bam Ya Rutsa A Tudun Biri, Kaduna 

Next Post

Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

Related

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn
Labarai

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

3 hours ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

9 hours ago
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
Labarai

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

11 hours ago
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu
Labarai

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

12 hours ago
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina
Labarai

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

13 hours ago
Next Post
Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

LABARAI MASU NASABA

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.