ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Kaduna Ta Fara Horas Da Malamai 8,500 Fasahar Kwamfuta A Fadin Jihar

by Sulaiman
3 years ago
Hukumar Ilimi

Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Jihar Kaduna, SUBEB ta kaddamar da horas da Malaman firamare 8,500 fasahar amfani da kwamfuta don inganta harkar karantarwa a fadin kananan hukumomi 23 da ke jihar.

Babbar Mamba a ofishin jin dadin ma’aikara ta SUBEB, Dr Christy Ayi Aladimerin ta taya Malaman murna da kasancewarsu daga cikin wadanda za su samu horon, inda ta ce, tana fatan za su yi amfani da Ilimin da suka samu ba don amfanin kashin kansu kadai ba har zuwa ga dalibansu.

  • Manoman Rani Za Su Samu Tallafin Noma Na Gwamnatin Tarayya Da Kashi 50 Cikin 100
  • Kowacce Yarinya Za Ta Samu Ilimi Da Sana’a A Jihar Katsina – Gwamnati

Ta kara da cewa, horaswar tana gudana ne a shiyyoyi Uku da ke fadin jihar – Zariya, Tsakiyar Kaduna da Kafanchan, kuma an zakulo Malaman ne daga duk Kananan hukumomin 23 da ke fadin jihar. Za a yi mako guda ana horas da Malaman inda aka fara daga yau Litinin 11 ga Watan Disamba,  2023.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, yayin da yake kaddamar da horas da Malaman, Babban Sakataren zartaswa na SUBEB, Alhaji Tijjani Abdullahi, ya ce, domin cika alkawurran da suka dauka na inganta bangaren ilimi, yasa suka shirya wannan horaswar a karkashin shirin (BESDA) ta yadda Malaman za su iya amfani da kwamfuta wajen bincike da kwarewa don amfanar dalibansu.

Hukumar Ilimi
Wasu daga cikin Malaman da suke amsa horo a dakin Kwamfuta na Jami’ar jihar Kadua.

Alhaji Tijjani ya bayyana amfanin sanin ilimin kwamfuta a wannan zamani da cewa, ya zama dole musamman a bangaren karantarwa. Ya kuma ja hankalin Malaman da su ci gaba da neman ilimin kwamfuta domin kara inganta karantarwarsu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Babban burin da muke son cimmawa a wannan horaswar da muka shiryawa Malamanmu shi ne, mu horas da su amfani da kwamfuta don karantar da dalibai, ta yadda za su iya bincike da neman kayan karatu a intanet.

Hukumar Ilimi
Dr Christy Ayi Aladimerin Permanent Member Human Resources, yayin da take jawabi ga mahalarta taron a dakin Kwamfuta da ke jami’ar KASU

“Da yawan Malaman da muke da su, za ka lura cewa, kamar suna tsoron taba kwamfuta, duk da cewa suna amfani da manyan salular zamani (Android). Don haka, muna fata Malaman, za su samu horo sosai a fannin amfani da kwamfuta don binciken sabbin kayan karantarwa.” Inji Tijjani

Daga karshe, Babban Sakataren, ya jaddada cewa, za su dunga gudanar da bincike a makarantu domin tabbatar da ganin Malaman suna amfanar Dalibai da Ilimin da suka samu.

Hukumar Ilimi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.