ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Kaduna Ta Fara Horas Da Malamai 8,500 Fasahar Kwamfuta A Fadin Jihar

by Sulaiman
2 years ago
Hukumar Ilimi

Hukumar Ilimi A Matakin Farko Ta Jihar Kaduna, SUBEB ta kaddamar da horas da Malaman firamare 8,500 fasahar amfani da kwamfuta don inganta harkar karantarwa a fadin kananan hukumomi 23 da ke jihar.

Babbar Mamba a ofishin jin dadin ma’aikara ta SUBEB, Dr Christy Ayi Aladimerin ta taya Malaman murna da kasancewarsu daga cikin wadanda za su samu horon, inda ta ce, tana fatan za su yi amfani da Ilimin da suka samu ba don amfanin kashin kansu kadai ba har zuwa ga dalibansu.

  • Manoman Rani Za Su Samu Tallafin Noma Na Gwamnatin Tarayya Da Kashi 50 Cikin 100
  • Kowacce Yarinya Za Ta Samu Ilimi Da Sana’a A Jihar Katsina – Gwamnati

Ta kara da cewa, horaswar tana gudana ne a shiyyoyi Uku da ke fadin jihar – Zariya, Tsakiyar Kaduna da Kafanchan, kuma an zakulo Malaman ne daga duk Kananan hukumomin 23 da ke fadin jihar. Za a yi mako guda ana horas da Malaman inda aka fara daga yau Litinin 11 ga Watan Disamba,  2023.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, yayin da yake kaddamar da horas da Malaman, Babban Sakataren zartaswa na SUBEB, Alhaji Tijjani Abdullahi, ya ce, domin cika alkawurran da suka dauka na inganta bangaren ilimi, yasa suka shirya wannan horaswar a karkashin shirin (BESDA) ta yadda Malaman za su iya amfani da kwamfuta wajen bincike da kwarewa don amfanar dalibansu.

Hukumar Ilimi
Wasu daga cikin Malaman da suke amsa horo a dakin Kwamfuta na Jami’ar jihar Kadua.

Alhaji Tijjani ya bayyana amfanin sanin ilimin kwamfuta a wannan zamani da cewa, ya zama dole musamman a bangaren karantarwa. Ya kuma ja hankalin Malaman da su ci gaba da neman ilimin kwamfuta domin kara inganta karantarwarsu.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Babban burin da muke son cimmawa a wannan horaswar da muka shiryawa Malamanmu shi ne, mu horas da su amfani da kwamfuta don karantar da dalibai, ta yadda za su iya bincike da neman kayan karatu a intanet.

Hukumar Ilimi
Dr Christy Ayi Aladimerin Permanent Member Human Resources, yayin da take jawabi ga mahalarta taron a dakin Kwamfuta da ke jami’ar KASU

“Da yawan Malaman da muke da su, za ka lura cewa, kamar suna tsoron taba kwamfuta, duk da cewa suna amfani da manyan salular zamani (Android). Don haka, muna fata Malaman, za su samu horo sosai a fannin amfani da kwamfuta don binciken sabbin kayan karantarwa.” Inji Tijjani

Daga karshe, Babban Sakataren, ya jaddada cewa, za su dunga gudanar da bincike a makarantu domin tabbatar da ganin Malaman suna amfanar Dalibai da Ilimin da suka samu.

Hukumar Ilimi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

Cinikin Motoci A Sin Ya Karu Da 27.4% A Watan Nuwamba

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.