Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS) da ma’aikatar harkokin tsaron cikin gida ta farin kaya (DSS) sun bayyana shirinsu na inganta hadin gwiwa don yaki da ta’addanci a kan iyakokin kasar musamman masu fasa-kwauri da safarar miyagun kwayoyi.
Wannan yunkurin ya biyo bayan tattaunawar da aka yi a ranar 6 ga Maris, 2025, tsakanin Kwanturola na yankin Oyo/Osun, Joseph Adelaja, da Daraktan DSS na jihar, Mista Rasheed Adelakun, a hedikwatar DSS ta jihar dake Ibadan, jihar Oyo.
- An Rufe Taro Na 3 Na Majalisar CPPCC Karo Na 14
- Kwallon Mata: Nijeriya Ta Nuna Wa Afrika Ta Kudu Kwanji A Pretoria
Sanarwar na kunshe ne a cikin wata sanarwa da NCS ta wallafa a shafinta na Twitter a ranar Litinin.
Adelaja ya jaddada mahimmancin ƙarfafa musayar bayanan sirri da haɗin gwiwar hukumomi, duba da irin kaifin basira da masu fasa-kwari ke amfani da wasu a ‘yan kwanakin nan wurin cimma muradunsu.
“Masu fasa kwauri na ci gaba da bunkasa a ayyukansu, kuma don tunkararsu yadda ya kamata, dole ne mu hada kai ta hanyar bayar da bayanan sirri don cimma nasarar ayyukanmu,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp