Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, an bayar da kwangilar aikin hanyoyin ruwa na Tashar Lekki.
Dantsoho ya bayyana haka ne, a cikin sanarwar da ya fitar bayan kai ziyarar aiki a Tashar ta Lekki, inda ya bayyana cewa, an bayar da wannan kwangilar ce, wadda kuma za gudanar da ita daidai da yin aikin na kasa da kasa.
- Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
- Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Ya sanar da cewa, wannan kwangilar za ta bamu abinda muke bukata na batun kara samar da hanyoyin ruwa a Tashar ta Lekki.
Kazalika, da yake yin tsokaci kan batun rage kudaden fito da Hukumar ta NPA ke karba a kan Jiragen ruwa, shugaban ya bayyana cewa, akasarin kayan aikin da NPA ta sawo, ta sawo ne, domin ta kara inganta ayyukanta, a daukacin Tashin Jiragen Ruwa na kasar, musamman domin Hukumar ta ga, ana biyan, dalolin kudade.
“Muna ci gaba da sayen kayan aiki, domin mu tabbatar da cewa, mun gudanar da ingantattun ayyuka, a daukacin Tashishin Jiragen Ruwan Kasar, domin daukacin kayan da muka sawo, mun sawo su ne, kan farashin dala,” Inji Shugaban.
Shugaban ya ci gaba da cewa, idan har zamu rage nauyin aikin da ke a kan Tashar ta Lekki, wajen biyan kudade, ya kamata ima Tashar ta san da cewa, muna da bukatar kudade da dama, domin mu sawo kayayyaki da dama na gudanar da ayyuka a Tashar, musamman domin mu tabbatar da cewa, ma’aikatan mu, na ci gaba da gudnar da ayyuakansu, a Tashar, kamar yadda ake bukata.
Dantso ya kara da cewa, za a yi aiki da tsarin NSW na kasa, inda zai samar da kaso 95 a cikin dari na gudanar da ayyuka a Tashar, wanda ya jaddada cewa, hakan zai kara rubunya, kudaden shiga, ga Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.
“Gudanar da hada-hadar kudade ta hanyar yin amfani da na’ura, zai kawar da biyan kadade ta hanyar yin amfani, da rasidan bayan kudade, a daukacin Tashohin Jiragen Ruwan kasar, “ A cewar Shugaban.
“Idan hakan ya wakana, muna da yakinin cewa, za mu kara samun kudaden samun kudaden shiga masu yawa, kuma ina tunanin, za mu duba yuwuar, rage kudin shigar na fiton Jiragen Ruwan, “ Inji Dantsoho.
Shugaban ya kuma yabawa mahukuntan na Tsahar ta Lekki, kan bayar da daukacin gudunmawar su, domin ganin an kara daga martabar Tashar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp