• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumomin Saudiyya Sun Kaddamar Da Taswirar Aikin Hajjin Shekarar 1445/2024

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar Hajji da Umrah ta kasar Saudiyya, a ranar Juma’a a birnin Makkah ta kaddamar da taswirar aikin hajjin shekarar 2024.

Ministan Hajji da Umrah na kasar Saudiyya, Dr Tawfiq Al Rabiah ne ya kaddamar da taswirar aikin a wani biki da ya samu halartar shuwagabanni da wakilan alhazai a kasar.

  • Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya
  • Halin Da Mahajjatan Nijeriya Suke Ciki A Saudiyya

Taron dai an yi shi ne domin nuna kawo karshen aikin Hajjin 2023.

Ya ce nan take za a fara shirye-shiryen Hajjin 2024 tare da mika wa kowace kasa da ta sanar da fara shirye-shiryen.

Al Rabiah ya kara da cewa za a kuma fitar da wasikun tabbatar da adadin maniyyata aikin hajjin 2024 ga kasashen da za su halarci aikin Hajjin.

Labarai Masu Nasaba

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

Ya jero abubuwan da suka fi daukar hankali a taswirar aikin hajjin 2014 da suka hada da gudanar da tarukan share fage daga ranar 16 ga watan Satumba zuwa 4 ga Nuwamba, da shirya taron karawa juna sani na kasa da kasa a ranar 8 ga Janairu, 2024.

Al Rabiah ya bayyana cewa aikin Hajji zai zama na farko da ya kammala dukkan shirye-shirye zai kuma sami damar zabar wurare a Masha’er (Mina, Arafat da Muzdalifah) don aikin Hajjin 2024.

Ministan ya mika godiyarsa ga dukkan hukumomi da ma’aikatan aikin hajji bisa rawar da suka taka a wannan aikin hajjin na shekarar 2023 tare da jaddada aniyar Hukumomin Saudiyya na yi wa Alhazai Bakin Allah hidima ta hanyar da ta dace da hanyar jin ra’ayi daga ma’aikatan aikin hajji da inganta ayyukanta.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa babban abin da ya faru a taron shi ne sanar da wadanda suka lashe lambar yabo ta Labbaikum Hajj Services a shekarar 2023 inda Iraki ta zama mafi kyawun shiri a aikin hajjin na shekarar 2023.

Sauran kasashe kamar Malaysia, Gambia, Bahrain, Singapore, Afirka ta Kudu da Azerbaijan sun yi fice a fannoni daban-daban na ayyukan hajji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin HajjiHajjHajjin 2024MadinahMakkahSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

Next Post

Sulhu Da ‘Yan bindiga Ne Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Yerima

Related

Kawayen amarya
Labarai

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

1 hour ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Labarai

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

3 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

5 hours ago
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
Labarai

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

14 hours ago
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
Labarai

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

14 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

15 hours ago
Next Post
Sulhu Da ‘Yan bindiga Ne Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Yerima

Sulhu Da 'Yan bindiga Ne Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya - Yerima

LABARAI MASU NASABA

Kawayen amarya

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.