ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Mahajjatan Nijeriya Suke Ciki A Saudiyya

by Abubakar Abba and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Mahajjatan Nijeriya

Hukumar jin dadin alhazai ta kasa (NAHCON) ta tabbatar da mutuwar mahajjacin Nijeriya a Makka da ke cikin Kasar Saudiyya.

Haka kuma ta bayyana cewa wasu mahajjaci guda daya ya bace a Madina, yayin da wasu mata guda uku suka yi barin ciki sakamakon wasu dadidai.

  • Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji

Shugaban tawagar likitocin hukumar, Dakta Usman Galadima shi ya bayyana hakan a wata tattaunawa ta musamman da ya yi da manema labarai. Ya ce likitoci guda shida na NAHCON ne ke duba majiyyatan Nijeriya 11,000 da suka samu raunika tun daga ranar da aka fara jigilar mahajjatan.

ADVERTISEMENT

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa wannan shi ne karo na farko da aka fi samun yawan mata masu juna biyu da suka isa kasa mai tsarki.

Hakazalika, Hukumar NAHCON ta nuna rashin jin dadinta kan zargin da wasu hukumomin aikin hajji na jihohin kasar suka yi mata kan gazawar tura kudi a cikin asusun gata na maniyyata masu aikin hajji bana wanda hakan ne ya sa wasu maniyyatan ba su samu damar tashi zuwa kasar Saudiyya ba domin sauke faradi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Mataimakin Darakantan samar da bayanai na NAHCON, Mousa Ubandawaki ne ya karyarta zargin hukumomin na jihohin a cikin sanarwar da ya fitar, inda sanarwar ta danganta zargin a matsayin marar tushe balle makama da da ake yi mata.

A cewar Ubandawaki, tun da farko hukumar ta amince da hukomomin kan cewa, kujerun da za a kebe wa maniyya za su kasance daga kashi 60 zuwa 40 a karkashin shirin na asusun gata na ajiyar kudin maniyyatan.

NAHCON ta nuna rashin jin dadinta kan zargin kin samarwa da maniyyan kujerun aikin hajjin bana a karkashina susun gata, inda hakan ya sa wasu hukumin aikin ajji na jihohin Kaduna, Abuja, Gombe da Jigawa suka zargi NAHCON.

Ubandawaki ya kara da cewa, yana da kyau a sanar da cewa Bakin Jaiz ya tura kudaden a cikin asusun gata na maniyyatan ga hukumomin aikin hajji na kasa don gudanar da aikin hajjin na bana.

Ya sanar da cewa, bisa wannan ana jiran hukumar aikin hajji ta Jihar Kaduna ta kebe kashi 40 a cikin dari wanda ya kai Naira 2,000 a cikin asusun gata na shirin.

Ubandawaki ya cewa, duk da wannan adadin maniyyatan, 108 kacal ne aka sanya su a cikin asusun gatan na Jihar Kaduna daga cikin maniyyata 6,255.

Acewarsa, duk irin wadannan matsalolin ne suka faru a sauran hukomomin aikin hajji da ke a sauran jihohin kasar nan, inda suka kitsa hakan don su bata wa NAHCON da shirin na asusun gata suna.

Ubandawaki ya baayyana cewa, hukmar ta ci gaba da nuna yin hakuri da fahimtar su kan shirin da kuma tsarin kafin kwalliya ta fara biya kudin Sabulu.

Ya sanar da cewa, bayanan da hukumar aikin hajji ta Jihar Kaduna ta sanar da sauran takwarorin na jihohi bisa zargin NAHCON karya ce tsagwaronta kuma sun yi hakan ne da nufin bata wa NAHCON suna.

NAHCON ta gode wa wadanda suka shiga cikin shirin na asusun gata, musamman kan yakinin da yardar da suka nuna kan shirin, inda hukumar ta kuma roki maniyyatan da ba a samu damar kwashe su zuwa Saudiyya ba, da su kwantar da hankulan su kuma zamo masu bin doka da oda.

Mahajjatan Nijeriya
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Mahajjatan Nijeriya
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.