• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumomin Sin Na Adawa Da Munanan Tanade-tanade Dake Da Alaka Da Sin A Cikin Dokar Ba Da Izinin Tsaron Amurka

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Hukumomin Sin Na Adawa Da Munanan Tanade-tanade Dake Da Alaka Da Sin A Cikin Dokar Ba Da Izinin Tsaron Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun kwamitin kula da harkokin waje na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC Xu Dong, ya bayyana rashin gamsuwa da rashin amincewa da kakkausar murya, kan munanan tanade-tanade dake da alaka da kasar Sin, a cikin dokar kasafin kudi ta shekarar 2024 mai nasaba da ba da iznin tsaron kasa ta Amurka, wacce kwanan nan aka sanyawa hannu.

Kakakin ya ce, kudirin da ke da alaka da wannan doka, yana magana ne kan batun yankin Taiwan, da ba da shawarar yin takara bisa manyan tsare-tsare da kasar Sin, da daukar Sin a matsayin barazana, da kuma yayata rage barazana a muhimman fannonin hulda da kasar Sin.

  • Hadin Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Zuba Jari Game Da Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ya Samu Ci Gaba Akai-Akai A Bana
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Gudanar Da Taron Tunawa Da Cika Shekaru 130 Da Haihuwar Mao Zedong

Ya bayyana cewa, hakan tamkar yin katsalandan ne ga harkokin cikin gidan kasar Sin matuka, da neman yin illa ga ‘yancin kai, da tsaro da ci gaban kasar Sin, kuma ya keta yarjejeniyar da shugabannin kasashen Sin da Amurka suka cimma a taron San Francisco.

Kakakin ya ce, batun yankin Taiwan, ainihin tushen moriyar kasar Sin ne, kana ginshikin tushen siyasa a alakar kasashen Sin da Amurka, kuma jan layi na farko da ba za a ketare ba a dangantakar kasashen biyu.
Ya kuma jaddada cewa, kasar Sin a ko yaushe tana bin hanyar samun ci gaba cikin lumana, kana tanade-tanaden Amurka sun yi watsi da gaskiya, suna kuma ba da shawarar mayar da wata kasa saniyar ware, da siyasantar da batutuwan da suka shafi tattalin arziki, da fasaha da al’adu bisa son rai, da kokarin dakile mu’amala da hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin da Amurka.
Xu ya ce, mutunta juna, zaman tare cikin lumana, da hadin gwiwar samun nasara tare, su ne alkiblar kokarin yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Amurka.

Sannan, kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Wu Qian, ya bayyana a yau Alhamis cewa, rundunar sojin kasar Sin ta nuna matukar rashin gamsuwa da kuma adawa da amincewar da Amurka ta yi da sanya hannu kan dokar ba da izinin tsaron kasa na shekarar kasafin kudi na 2024, wanda ke kunshe da abubuwan da ba su dace ba da suka shafi kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Wu ya ce, wannan mataki da suka dauka ba tare da wata hujja ba akan abin da suke kira “barazanar sojin kasar Sin” katsalandan ne ga harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma yana yin illa sosai ga ‘yanci kai, da tsaro da ci gaban kasar Sin. (Ibrahim Yaya, Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamishinan Samar Da Ababen More Rayuwa Na Ondo Ya Yi Murabus

Next Post

INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

20 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

21 hours ago
Next Post
inec

INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.