ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumomin Sin Na Adawa Da Munanan Tanade-tanade Dake Da Alaka Da Sin A Cikin Dokar Ba Da Izinin Tsaron Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Mai magana da yawun kwamitin kula da harkokin waje na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC Xu Dong, ya bayyana rashin gamsuwa da rashin amincewa da kakkausar murya, kan munanan tanade-tanade dake da alaka da kasar Sin, a cikin dokar kasafin kudi ta shekarar 2024 mai nasaba da ba da iznin tsaron kasa ta Amurka, wacce kwanan nan aka sanyawa hannu.

Kakakin ya ce, kudirin da ke da alaka da wannan doka, yana magana ne kan batun yankin Taiwan, da ba da shawarar yin takara bisa manyan tsare-tsare da kasar Sin, da daukar Sin a matsayin barazana, da kuma yayata rage barazana a muhimman fannonin hulda da kasar Sin.

  • Hadin Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Zuba Jari Game Da Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ya Samu Ci Gaba Akai-Akai A Bana
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Gudanar Da Taron Tunawa Da Cika Shekaru 130 Da Haihuwar Mao Zedong

Ya bayyana cewa, hakan tamkar yin katsalandan ne ga harkokin cikin gidan kasar Sin matuka, da neman yin illa ga ‘yancin kai, da tsaro da ci gaban kasar Sin, kuma ya keta yarjejeniyar da shugabannin kasashen Sin da Amurka suka cimma a taron San Francisco.

ADVERTISEMENT

Kakakin ya ce, batun yankin Taiwan, ainihin tushen moriyar kasar Sin ne, kana ginshikin tushen siyasa a alakar kasashen Sin da Amurka, kuma jan layi na farko da ba za a ketare ba a dangantakar kasashen biyu.
Ya kuma jaddada cewa, kasar Sin a ko yaushe tana bin hanyar samun ci gaba cikin lumana, kana tanade-tanaden Amurka sun yi watsi da gaskiya, suna kuma ba da shawarar mayar da wata kasa saniyar ware, da siyasantar da batutuwan da suka shafi tattalin arziki, da fasaha da al’adu bisa son rai, da kokarin dakile mu’amala da hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin da Amurka.
Xu ya ce, mutunta juna, zaman tare cikin lumana, da hadin gwiwar samun nasara tare, su ne alkiblar kokarin yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Amurka.

Sannan, kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Wu Qian, ya bayyana a yau Alhamis cewa, rundunar sojin kasar Sin ta nuna matukar rashin gamsuwa da kuma adawa da amincewar da Amurka ta yi da sanya hannu kan dokar ba da izinin tsaron kasa na shekarar kasafin kudi na 2024, wanda ke kunshe da abubuwan da ba su dace ba da suka shafi kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Wu ya ce, wannan mataki da suka dauka ba tare da wata hujja ba akan abin da suke kira “barazanar sojin kasar Sin” katsalandan ne ga harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma yana yin illa sosai ga ‘yanci kai, da tsaro da ci gaban kasar Sin. (Ibrahim Yaya, Muhammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
Daga Birnin Sin

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
Next Post
inec

INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.