ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumomin Sin Na Adawa Da Munanan Tanade-tanade Dake Da Alaka Da Sin A Cikin Dokar Ba Da Izinin Tsaron Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Mai magana da yawun kwamitin kula da harkokin waje na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC Xu Dong, ya bayyana rashin gamsuwa da rashin amincewa da kakkausar murya, kan munanan tanade-tanade dake da alaka da kasar Sin, a cikin dokar kasafin kudi ta shekarar 2024 mai nasaba da ba da iznin tsaron kasa ta Amurka, wacce kwanan nan aka sanyawa hannu.

Kakakin ya ce, kudirin da ke da alaka da wannan doka, yana magana ne kan batun yankin Taiwan, da ba da shawarar yin takara bisa manyan tsare-tsare da kasar Sin, da daukar Sin a matsayin barazana, da kuma yayata rage barazana a muhimman fannonin hulda da kasar Sin.

  • Hadin Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Zuba Jari Game Da Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ya Samu Ci Gaba Akai-Akai A Bana
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Gudanar Da Taron Tunawa Da Cika Shekaru 130 Da Haihuwar Mao Zedong

Ya bayyana cewa, hakan tamkar yin katsalandan ne ga harkokin cikin gidan kasar Sin matuka, da neman yin illa ga ‘yancin kai, da tsaro da ci gaban kasar Sin, kuma ya keta yarjejeniyar da shugabannin kasashen Sin da Amurka suka cimma a taron San Francisco.

ADVERTISEMENT

Kakakin ya ce, batun yankin Taiwan, ainihin tushen moriyar kasar Sin ne, kana ginshikin tushen siyasa a alakar kasashen Sin da Amurka, kuma jan layi na farko da ba za a ketare ba a dangantakar kasashen biyu.
Ya kuma jaddada cewa, kasar Sin a ko yaushe tana bin hanyar samun ci gaba cikin lumana, kana tanade-tanaden Amurka sun yi watsi da gaskiya, suna kuma ba da shawarar mayar da wata kasa saniyar ware, da siyasantar da batutuwan da suka shafi tattalin arziki, da fasaha da al’adu bisa son rai, da kokarin dakile mu’amala da hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin da Amurka.
Xu ya ce, mutunta juna, zaman tare cikin lumana, da hadin gwiwar samun nasara tare, su ne alkiblar kokarin yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Amurka.

Sannan, kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Wu Qian, ya bayyana a yau Alhamis cewa, rundunar sojin kasar Sin ta nuna matukar rashin gamsuwa da kuma adawa da amincewar da Amurka ta yi da sanya hannu kan dokar ba da izinin tsaron kasa na shekarar kasafin kudi na 2024, wanda ke kunshe da abubuwan da ba su dace ba da suka shafi kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Wu ya ce, wannan mataki da suka dauka ba tare da wata hujja ba akan abin da suke kira “barazanar sojin kasar Sin” katsalandan ne ga harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma yana yin illa sosai ga ‘yanci kai, da tsaro da ci gaban kasar Sin. (Ibrahim Yaya, Muhammed Yahaya)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
inec

INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.