ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IBB Na Kokarin Kawo Karshen Sabanin Da Ke Tsakanin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan 5 

* Lamarin ya zo daidai da fatan da Atikun ke yi wa 'Yan 5 din na maraba da dinke sabanin da ke tsakaninsu.

by Muhammad
3 years ago
Da

Alamu masu karfi na nuna cewa tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), zai iya shiga cikin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar adawa ta PDP.

LEADERSHIP ta rawaito cewa tsohon shugaban na Nijeriya zai yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, da kuma wasu gwamnonin jam’iyyar biyar da aka fi sani da G-5 a Minna, babban birnin jihar Neja ranar Juma’a.

  • Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku
  • Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

Ganawar na zuwa ne kwanaki uku bayan da IBB ya kuma karbi bakuncin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da tawagarsa a gidansa da ke Minna.

ADVERTISEMENT

Majiyoyi sun nuna cewa matakin na baya-bayan nan na sasantawa kan shigar IBB, da alamun wani tsohon babban jami’in leken asiri na soja ne da wasu masu ruwa da tsaki daga Arewa masu goyon bayan Atiku ne suka shirya hakan.

A wani labarin kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya mayar da martani ga kalaman da aka jiyo shugaban G-5 kuma gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya yi yayin ganawa da manema labarai a jihar Bauchi kwanakin baya, inda ya ce kungiyar tana nan daram kuma kofa a bude don yin sulhu.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

A cikin wata takardar manema labarai da aka akalanta ta da, ‘Atikun, an jiyo cewa yana maraba da samun zaman lafiya da kungiyar ta Wike’ wanda mai baiwa Atiku shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya sanya wa hannu, wadda LEADERSHIP ta samu a ranar Juma’a.

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriyar ya yi na’am da rahotannin da ke cewa Gwamna Wike da kungiyarsa sun yi na’am da su warware matsalolin da shi.

“Atiku Abubakar ya kuma bayyana kudurinsa na yin shawarwarin da za a warware rikicin bisa amana da kuma share fagen samun karin karfi da hadin kan PDP.

“Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya ya lura cewa ba a taba rufe kofofin sulhu da Gwamna Wike da kungiyarsa a kowane lokaci ba.

“Ya kuma umurci kowane shugaban jam’iyyar da magoya bayansu ba tare da la’akari da ra’ayinsu ba da su kasance masu bude ido tare da marawa tsarin warware matsalolin da ke faruwa,” in ji Ibe.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jam’iyyar PDP tsagin G-5 ta yi ta takun-saka da Atiku da shugabannin PDP tun bayan fitowar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023, kan ci gaba da zaman Dr. Iyorchia Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Next Post
Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.