• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IBB Na Kokarin Kawo Karshen Sabanin Da Ke Tsakanin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan 5 

* Lamarin ya zo daidai da fatan da Atikun ke yi wa 'Yan 5 din na maraba da dinke sabanin da ke tsakaninsu.

by Muhammad
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Na Amince Zan Goyi Bayan Takarar Atiku Abubakar —Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alamu masu karfi na nuna cewa tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), zai iya shiga cikin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar adawa ta PDP.

LEADERSHIP ta rawaito cewa tsohon shugaban na Nijeriya zai yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, da kuma wasu gwamnonin jam’iyyar biyar da aka fi sani da G-5 a Minna, babban birnin jihar Neja ranar Juma’a.

  • Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku
  • Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

Ganawar na zuwa ne kwanaki uku bayan da IBB ya kuma karbi bakuncin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da tawagarsa a gidansa da ke Minna.

Majiyoyi sun nuna cewa matakin na baya-bayan nan na sasantawa kan shigar IBB, da alamun wani tsohon babban jami’in leken asiri na soja ne da wasu masu ruwa da tsaki daga Arewa masu goyon bayan Atiku ne suka shirya hakan.

A wani labarin kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya mayar da martani ga kalaman da aka jiyo shugaban G-5 kuma gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya yi yayin ganawa da manema labarai a jihar Bauchi kwanakin baya, inda ya ce kungiyar tana nan daram kuma kofa a bude don yin sulhu.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

A cikin wata takardar manema labarai da aka akalanta ta da, ‘Atikun, an jiyo cewa yana maraba da samun zaman lafiya da kungiyar ta Wike’ wanda mai baiwa Atiku shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya sanya wa hannu, wadda LEADERSHIP ta samu a ranar Juma’a.

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriyar ya yi na’am da rahotannin da ke cewa Gwamna Wike da kungiyarsa sun yi na’am da su warware matsalolin da shi.

“Atiku Abubakar ya kuma bayyana kudurinsa na yin shawarwarin da za a warware rikicin bisa amana da kuma share fagen samun karin karfi da hadin kan PDP.

“Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya ya lura cewa ba a taba rufe kofofin sulhu da Gwamna Wike da kungiyarsa a kowane lokaci ba.

“Ya kuma umurci kowane shugaban jam’iyyar da magoya bayansu ba tare da la’akari da ra’ayinsu ba da su kasance masu bude ido tare da marawa tsarin warware matsalolin da ke faruwa,” in ji Ibe.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jam’iyyar PDP tsagin G-5 ta yi ta takun-saka da Atiku da shugabannin PDP tun bayan fitowar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023, kan ci gaba da zaman Dr. Iyorchia Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Doguwa Da Garo: Yadda Siyasar Kano Ta Dauki Sabon Salo

Next Post

Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

Related

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

5 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

7 days ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

2 weeks ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

4 weeks ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

1 month ago
Ku Gafarce Ni, Na Yi Nadamar Tallata Tinubu Da Na Yi – Ɗanbilki Kwamanda
Da ɗumi-ɗuminsa

Ku Gafarce Ni, Na Yi Nadamar Tallata Tinubu Da Na Yi – Ɗanbilki Kwamanda

3 months ago
Next Post
Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.