• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IBB Na Kokarin Kawo Karshen Sabanin Da Ke Tsakanin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan 5 

* Lamarin ya zo daidai da fatan da Atikun ke yi wa 'Yan 5 din na maraba da dinke sabanin da ke tsakaninsu.

by Muhammad
3 years ago
Da

Alamu masu karfi na nuna cewa tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), zai iya shiga cikin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar adawa ta PDP.

LEADERSHIP ta rawaito cewa tsohon shugaban na Nijeriya zai yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, da kuma wasu gwamnonin jam’iyyar biyar da aka fi sani da G-5 a Minna, babban birnin jihar Neja ranar Juma’a.

  • Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku
  • Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

Ganawar na zuwa ne kwanaki uku bayan da IBB ya kuma karbi bakuncin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da tawagarsa a gidansa da ke Minna.

Majiyoyi sun nuna cewa matakin na baya-bayan nan na sasantawa kan shigar IBB, da alamun wani tsohon babban jami’in leken asiri na soja ne da wasu masu ruwa da tsaki daga Arewa masu goyon bayan Atiku ne suka shirya hakan.

A wani labarin kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya mayar da martani ga kalaman da aka jiyo shugaban G-5 kuma gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya yi yayin ganawa da manema labarai a jihar Bauchi kwanakin baya, inda ya ce kungiyar tana nan daram kuma kofa a bude don yin sulhu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

A cikin wata takardar manema labarai da aka akalanta ta da, ‘Atikun, an jiyo cewa yana maraba da samun zaman lafiya da kungiyar ta Wike’ wanda mai baiwa Atiku shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya sanya wa hannu, wadda LEADERSHIP ta samu a ranar Juma’a.

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriyar ya yi na’am da rahotannin da ke cewa Gwamna Wike da kungiyarsa sun yi na’am da su warware matsalolin da shi.

“Atiku Abubakar ya kuma bayyana kudurinsa na yin shawarwarin da za a warware rikicin bisa amana da kuma share fagen samun karin karfi da hadin kan PDP.

“Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya ya lura cewa ba a taba rufe kofofin sulhu da Gwamna Wike da kungiyarsa a kowane lokaci ba.

“Ya kuma umurci kowane shugaban jam’iyyar da magoya bayansu ba tare da la’akari da ra’ayinsu ba da su kasance masu bude ido tare da marawa tsarin warware matsalolin da ke faruwa,” in ji Ibe.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jam’iyyar PDP tsagin G-5 ta yi ta takun-saka da Atiku da shugabannin PDP tun bayan fitowar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023, kan ci gaba da zaman Dr. Iyorchia Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

October 1, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Next Post
Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.