ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IBB Na Kokarin Kawo Karshen Sabanin Da Ke Tsakanin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan 5 

* Lamarin ya zo daidai da fatan da Atikun ke yi wa 'Yan 5 din na maraba da dinke sabanin da ke tsakaninsu.

by Muhammad
4 years ago
Da

Alamu masu karfi na nuna cewa tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), zai iya shiga cikin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar adawa ta PDP.

LEADERSHIP ta rawaito cewa tsohon shugaban na Nijeriya zai yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, da kuma wasu gwamnonin jam’iyyar biyar da aka fi sani da G-5 a Minna, babban birnin jihar Neja ranar Juma’a.

  • Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku
  • Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

Ganawar na zuwa ne kwanaki uku bayan da IBB ya kuma karbi bakuncin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da tawagarsa a gidansa da ke Minna.

ADVERTISEMENT

Majiyoyi sun nuna cewa matakin na baya-bayan nan na sasantawa kan shigar IBB, da alamun wani tsohon babban jami’in leken asiri na soja ne da wasu masu ruwa da tsaki daga Arewa masu goyon bayan Atiku ne suka shirya hakan.

A wani labarin kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya mayar da martani ga kalaman da aka jiyo shugaban G-5 kuma gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya yi yayin ganawa da manema labarai a jihar Bauchi kwanakin baya, inda ya ce kungiyar tana nan daram kuma kofa a bude don yin sulhu.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

A cikin wata takardar manema labarai da aka akalanta ta da, ‘Atikun, an jiyo cewa yana maraba da samun zaman lafiya da kungiyar ta Wike’ wanda mai baiwa Atiku shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya sanya wa hannu, wadda LEADERSHIP ta samu a ranar Juma’a.

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriyar ya yi na’am da rahotannin da ke cewa Gwamna Wike da kungiyarsa sun yi na’am da su warware matsalolin da shi.

“Atiku Abubakar ya kuma bayyana kudurinsa na yin shawarwarin da za a warware rikicin bisa amana da kuma share fagen samun karin karfi da hadin kan PDP.

“Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya ya lura cewa ba a taba rufe kofofin sulhu da Gwamna Wike da kungiyarsa a kowane lokaci ba.

“Ya kuma umurci kowane shugaban jam’iyyar da magoya bayansu ba tare da la’akari da ra’ayinsu ba da su kasance masu bude ido tare da marawa tsarin warware matsalolin da ke faruwa,” in ji Ibe.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jam’iyyar PDP tsagin G-5 ta yi ta takun-saka da Atiku da shugabannin PDP tun bayan fitowar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023, kan ci gaba da zaman Dr. Iyorchia Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.

Da
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Next Post
Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.