• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

by Khalid Idris Doya
2 years ago
NITDA

Shugaban hukumar yaki da rashawa da dangoginta (ICPC) na jagorantar hadin guiwa da hukumar bunkasa fasahar sadarwa ta kasa (NITDA) wajen yin amfani da fasahar zamani domin dakilewa da toshe kafofin rashawa da babakere da dukiyar al’umma a Nijeriya.

Shugaban ICPC, Musa Aliyu, SAN, a yayin zaman domin kulla kyakkyawar alakar aiki da NITDA da ya gudana a cikin makon jiya, ya ce, babu makawa, rungumar dabarun amfani da hanyoyin fasaha na zamani za su taimaka sosai wajen rage kaifin rashawa a kasar nan.

  • Zargin Badaƙala: Sadiya Ta Kai Kanta Ofishin EFCC
  • Kotu Ta Dakatar Da EFCC, ICPC, DSS Daga Tsare Sanata Yari

Ganawar ta kuma kai ga bada daman hada wata kakkarfar kwamiti da zai kara kyautata alaka a tsakanin hukumomin biyu, wanda a cewar masu ruwa da tsakin, wani mataki ne bullo da sabbin dabarun zamani da hikimomi wajen magance illa da barnar rashawa da cin hanci a Nijeriya.

Shafin Kimiyya da fasaha na LEADERSHIP Hausa ya labarto cewa, ita dai wannan alakar an shirya da tsarata ne tun zamanin mulkin tsohon shugaban ICPC, Farfesa Bolaji Owasanoye, a 2021 da nufin taimakawa kokarinsu wajen yaki da rashawa da toshe haramtatun hanyoyin hada-hadar kudade.

A sanarwar manema labarai da kakakin ICPC Azuka Ogugua ya fitar, ya ce, shugaban ICPC na yanzu, Aliyu ya ziyarci NITDA ne domin tsara sabbin dabarun yaki da rashawa, maida hankali wajen amfani da fasaha domin jagorantar nasarorin ayyukan ICPC kan yaki da rashawa da cin hanci.

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Aliyu na cewa, “Da dukkanin amfanun kowace bangare, rungumar dabarun fasaha shi ne muhimman matakin yaki da kuma dakile rashawa. Alakarmu da NITDA na da manufar taimakawa ICPC ne wajen tafiya da zamani, inganta gaskiya, rikon amana, dakile kafofin barnata dukiyar jama’a da kuma inganta amincewar jama’a ga masu jagorantarsu ta hanyar rage kaifin rashawa.

“Yaki da rashawa ba tare da amfani da fasaha ba ba zai yiyu ba a wannan lokacin. Babban nauyin da ke kan ICPC sun hada da har da dakile aikata rashawa, bincike, da gurfanawa. Fasaha zai taimaka mana sosai wajen gudanar da wadannan ayyukan da suke gabanmu,” shugaban ICPC ya shaida.

Shi kuma a nasa bangaren, darakta janar na NITDA, Kashifu Abdullahi, ya nuna kwarin guiwarsu na taimaka wa ICPC wajen cimma manufofin kyautata aiki da ta sanya a gaba.

Ya nanata muhimmancin da ke akwai wajen saukaka aiki da kyautata aikin ta hanyar amfani da fasaha, ya ce, za su kara zaunawa su bullo da muhimman hanyoyin da za su taimaka wa hukumar matuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.