ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NITDA

Shugaban hukumar yaki da rashawa da dangoginta (ICPC) na jagorantar hadin guiwa da hukumar bunkasa fasahar sadarwa ta kasa (NITDA) wajen yin amfani da fasahar zamani domin dakilewa da toshe kafofin rashawa da babakere da dukiyar al’umma a Nijeriya.

Shugaban ICPC, Musa Aliyu, SAN, a yayin zaman domin kulla kyakkyawar alakar aiki da NITDA da ya gudana a cikin makon jiya, ya ce, babu makawa, rungumar dabarun amfani da hanyoyin fasaha na zamani za su taimaka sosai wajen rage kaifin rashawa a kasar nan.

  • Zargin Badaƙala: Sadiya Ta Kai Kanta Ofishin EFCC
  • Kotu Ta Dakatar Da EFCC, ICPC, DSS Daga Tsare Sanata Yari

Ganawar ta kuma kai ga bada daman hada wata kakkarfar kwamiti da zai kara kyautata alaka a tsakanin hukumomin biyu, wanda a cewar masu ruwa da tsakin, wani mataki ne bullo da sabbin dabarun zamani da hikimomi wajen magance illa da barnar rashawa da cin hanci a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Shafin Kimiyya da fasaha na LEADERSHIP Hausa ya labarto cewa, ita dai wannan alakar an shirya da tsarata ne tun zamanin mulkin tsohon shugaban ICPC, Farfesa Bolaji Owasanoye, a 2021 da nufin taimakawa kokarinsu wajen yaki da rashawa da toshe haramtatun hanyoyin hada-hadar kudade.

A sanarwar manema labarai da kakakin ICPC Azuka Ogugua ya fitar, ya ce, shugaban ICPC na yanzu, Aliyu ya ziyarci NITDA ne domin tsara sabbin dabarun yaki da rashawa, maida hankali wajen amfani da fasaha domin jagorantar nasarorin ayyukan ICPC kan yaki da rashawa da cin hanci.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Aliyu na cewa, “Da dukkanin amfanun kowace bangare, rungumar dabarun fasaha shi ne muhimman matakin yaki da kuma dakile rashawa. Alakarmu da NITDA na da manufar taimakawa ICPC ne wajen tafiya da zamani, inganta gaskiya, rikon amana, dakile kafofin barnata dukiyar jama’a da kuma inganta amincewar jama’a ga masu jagorantarsu ta hanyar rage kaifin rashawa.

“Yaki da rashawa ba tare da amfani da fasaha ba ba zai yiyu ba a wannan lokacin. Babban nauyin da ke kan ICPC sun hada da har da dakile aikata rashawa, bincike, da gurfanawa. Fasaha zai taimaka mana sosai wajen gudanar da wadannan ayyukan da suke gabanmu,” shugaban ICPC ya shaida.

Shi kuma a nasa bangaren, darakta janar na NITDA, Kashifu Abdullahi, ya nuna kwarin guiwarsu na taimaka wa ICPC wajen cimma manufofin kyautata aiki da ta sanya a gaba.

Ya nanata muhimmancin da ke akwai wajen saukaka aiki da kyautata aikin ta hanyar amfani da fasaha, ya ce, za su kara zaunawa su bullo da muhimman hanyoyin da za su taimaka wa hukumar matuka.

NITDA
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.