ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

by Khalid Idris Doya
2 years ago
NITDA

Shugaban hukumar yaki da rashawa da dangoginta (ICPC) na jagorantar hadin guiwa da hukumar bunkasa fasahar sadarwa ta kasa (NITDA) wajen yin amfani da fasahar zamani domin dakilewa da toshe kafofin rashawa da babakere da dukiyar al’umma a Nijeriya.

Shugaban ICPC, Musa Aliyu, SAN, a yayin zaman domin kulla kyakkyawar alakar aiki da NITDA da ya gudana a cikin makon jiya, ya ce, babu makawa, rungumar dabarun amfani da hanyoyin fasaha na zamani za su taimaka sosai wajen rage kaifin rashawa a kasar nan.

  • Zargin Badaƙala: Sadiya Ta Kai Kanta Ofishin EFCC
  • Kotu Ta Dakatar Da EFCC, ICPC, DSS Daga Tsare Sanata Yari

Ganawar ta kuma kai ga bada daman hada wata kakkarfar kwamiti da zai kara kyautata alaka a tsakanin hukumomin biyu, wanda a cewar masu ruwa da tsakin, wani mataki ne bullo da sabbin dabarun zamani da hikimomi wajen magance illa da barnar rashawa da cin hanci a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Shafin Kimiyya da fasaha na LEADERSHIP Hausa ya labarto cewa, ita dai wannan alakar an shirya da tsarata ne tun zamanin mulkin tsohon shugaban ICPC, Farfesa Bolaji Owasanoye, a 2021 da nufin taimakawa kokarinsu wajen yaki da rashawa da toshe haramtatun hanyoyin hada-hadar kudade.

A sanarwar manema labarai da kakakin ICPC Azuka Ogugua ya fitar, ya ce, shugaban ICPC na yanzu, Aliyu ya ziyarci NITDA ne domin tsara sabbin dabarun yaki da rashawa, maida hankali wajen amfani da fasaha domin jagorantar nasarorin ayyukan ICPC kan yaki da rashawa da cin hanci.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Aliyu na cewa, “Da dukkanin amfanun kowace bangare, rungumar dabarun fasaha shi ne muhimman matakin yaki da kuma dakile rashawa. Alakarmu da NITDA na da manufar taimakawa ICPC ne wajen tafiya da zamani, inganta gaskiya, rikon amana, dakile kafofin barnata dukiyar jama’a da kuma inganta amincewar jama’a ga masu jagorantarsu ta hanyar rage kaifin rashawa.

“Yaki da rashawa ba tare da amfani da fasaha ba ba zai yiyu ba a wannan lokacin. Babban nauyin da ke kan ICPC sun hada da har da dakile aikata rashawa, bincike, da gurfanawa. Fasaha zai taimaka mana sosai wajen gudanar da wadannan ayyukan da suke gabanmu,” shugaban ICPC ya shaida.

Shi kuma a nasa bangaren, darakta janar na NITDA, Kashifu Abdullahi, ya nuna kwarin guiwarsu na taimaka wa ICPC wajen cimma manufofin kyautata aiki da ta sanya a gaba.

Ya nanata muhimmancin da ke akwai wajen saukaka aiki da kyautata aikin ta hanyar amfani da fasaha, ya ce, za su kara zaunawa su bullo da muhimman hanyoyin da za su taimaka wa hukumar matuka.

NITDA
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

Bangaren Cinikayyar Waje Na Sin Ya Samu Babban Sakamako A 2023

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.