• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

by Sulaiman and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Labarai
0
ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC ta fara binciken tabbatar da matsayin aiwatar da ayyuka a Mazabun Majalisar Tarayya 10 wadanda Gwamnatin Tarayya ta bayar da kwangilar aiwatar da su kan sama da naira miliyan 355 a Sakkwato.

Binciken gano matsayin ayyukan yana a karkashin rukuni na biyar na bankado ayyukan Mazabun Tarayya da Hukumar ICPC ke aiwatarwa a Jihohi 21 wadanda aka bayar da aikin su a cikin Kasafin Kudin 2021.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da ‘Yan Tawagar Biki 50 A Hanyar Zamfara Zuwa Sokoto

Jagoran tagagar Hukumar ICPC Mista Sa’idu Yahaya ya bayyanawa manema labarai a yau cewar za su gudanar da binciken ayyuka a yankin Majalisar Dattawa biyu da Mazabun ‘Yan Majalisar Tarayya biyar. Daga ciki akwai Mazabar Sakkwato ta Arewa wadda Sanata Aliyu Wamakko, Mataimakin Shugaban Kwamitin Yaki da Rashawa a Majalisar Dattawa ke wakilta.

“An bayar da kwangilar ayyukan a kan naira miliyan 355, 391, 657. 95 tare da tsammanin za a kammala su bakidaya. Tawagar mu ta kunshi wakilan ICPC, kungiyoyin farar hula da ‘yan jarida wadanda duka za su bi diddigin ayyukan.”

“Hakan na da manufar gano ayyukan, yanayin ayyukan da adadin kudin da aka kashe a ayyukan da adadin kudin kwangila, ‘yan kwangila, kudaden da aka biya da gano mutanen da suka jagoranci ayyukan.” Ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

A cewarsa tawagar za ta kuma binciko kamfunan da suka yi ayyukan, binciken ko an cika sharuddan ayyukan da kudaden haraji. Ya ce za su duba kima da muhimmancin ayyukan ga al’ummar da aka yi domin su.

Ayyukan da za a gudanar da binciken gano su sun hada da samar da motoci a yankin Majalisar Dattawa a Sakkwato ta Gabas da Sanata Ibrahim Abdullahi Gobir ke wakilta da babura a Mazabar Sakkwato ta Arewa da Sanata Aliyu Wamakko, tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato ke wakilta.

Haka ma akwai binciken gano tabbatar da rarraba babura 188 a Mazabar Gwadabawa/Illela da Hon. Abdullahi Salame ke wakilta a Majalisar Wakilai.

Sauran sun hada da samar da takin zamani na NPK da fanfunan ruwa a Mazabar Kware/Wamakko da shirin karfafawa al’umma kan aikin gona a Mazabar Tarayya ta Bodinga/Dange/Shuni/Tureta wadda Hon. Balarabe Kakale ke wakilta a wa’adin zango na farko.

Tawagar ta riga ta ziyarci wasu daga cikin ayyukan da aka aiwatar a Mazabar Tarayya ta Sakkwato ta Arewa/Sakkwato ta Kudu da Bodinga/Dange/Shuni/Tureta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

Next Post

Gwamnatin APC Ta Yaudari ‘Yan Nijeriya – Kwankwaso

Related

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da É—umi-É—uminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

3 minutes ago
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

3 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

4 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

6 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

7 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

15 hours ago
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Gwamnatin APC Ta Yaudari 'Yan Nijeriya - Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.