• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

by Sulaiman and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
ICPC

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC ta fara binciken tabbatar da matsayin aiwatar da ayyuka a Mazabun Majalisar Tarayya 10 wadanda Gwamnatin Tarayya ta bayar da kwangilar aiwatar da su kan sama da naira miliyan 355 a Sakkwato.

Binciken gano matsayin ayyukan yana a karkashin rukuni na biyar na bankado ayyukan Mazabun Tarayya da Hukumar ICPC ke aiwatarwa a Jihohi 21 wadanda aka bayar da aikin su a cikin Kasafin Kudin 2021.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da ‘Yan Tawagar Biki 50 A Hanyar Zamfara Zuwa Sokoto

Jagoran tagagar Hukumar ICPC Mista Sa’idu Yahaya ya bayyanawa manema labarai a yau cewar za su gudanar da binciken ayyuka a yankin Majalisar Dattawa biyu da Mazabun ‘Yan Majalisar Tarayya biyar. Daga ciki akwai Mazabar Sakkwato ta Arewa wadda Sanata Aliyu Wamakko, Mataimakin Shugaban Kwamitin Yaki da Rashawa a Majalisar Dattawa ke wakilta.

“An bayar da kwangilar ayyukan a kan naira miliyan 355, 391, 657. 95 tare da tsammanin za a kammala su bakidaya. Tawagar mu ta kunshi wakilan ICPC, kungiyoyin farar hula da ‘yan jarida wadanda duka za su bi diddigin ayyukan.”

“Hakan na da manufar gano ayyukan, yanayin ayyukan da adadin kudin da aka kashe a ayyukan da adadin kudin kwangila, ‘yan kwangila, kudaden da aka biya da gano mutanen da suka jagoranci ayyukan.” Ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A cewarsa tawagar za ta kuma binciko kamfunan da suka yi ayyukan, binciken ko an cika sharuddan ayyukan da kudaden haraji. Ya ce za su duba kima da muhimmancin ayyukan ga al’ummar da aka yi domin su.

Ayyukan da za a gudanar da binciken gano su sun hada da samar da motoci a yankin Majalisar Dattawa a Sakkwato ta Gabas da Sanata Ibrahim Abdullahi Gobir ke wakilta da babura a Mazabar Sakkwato ta Arewa da Sanata Aliyu Wamakko, tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato ke wakilta.

Haka ma akwai binciken gano tabbatar da rarraba babura 188 a Mazabar Gwadabawa/Illela da Hon. Abdullahi Salame ke wakilta a Majalisar Wakilai.

Sauran sun hada da samar da takin zamani na NPK da fanfunan ruwa a Mazabar Kware/Wamakko da shirin karfafawa al’umma kan aikin gona a Mazabar Tarayya ta Bodinga/Dange/Shuni/Tureta wadda Hon. Balarabe Kakale ke wakilta a wa’adin zango na farko.

Tawagar ta riga ta ziyarci wasu daga cikin ayyukan da aka aiwatar a Mazabar Tarayya ta Sakkwato ta Arewa/Sakkwato ta Kudu da Bodinga/Dange/Shuni/Tureta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)
Labarai

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Gwamnatin APC Ta Yaudari 'Yan Nijeriya - Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legas

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.