• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

by Sulaiman and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Labarai
0
ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC ta fara binciken tabbatar da matsayin aiwatar da ayyuka a Mazabun Majalisar Tarayya 10 wadanda Gwamnatin Tarayya ta bayar da kwangilar aiwatar da su kan sama da naira miliyan 355 a Sakkwato.

Binciken gano matsayin ayyukan yana a karkashin rukuni na biyar na bankado ayyukan Mazabun Tarayya da Hukumar ICPC ke aiwatarwa a Jihohi 21 wadanda aka bayar da aikin su a cikin Kasafin Kudin 2021.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da ‘Yan Tawagar Biki 50 A Hanyar Zamfara Zuwa Sokoto

Jagoran tagagar Hukumar ICPC Mista Sa’idu Yahaya ya bayyanawa manema labarai a yau cewar za su gudanar da binciken ayyuka a yankin Majalisar Dattawa biyu da Mazabun ‘Yan Majalisar Tarayya biyar. Daga ciki akwai Mazabar Sakkwato ta Arewa wadda Sanata Aliyu Wamakko, Mataimakin Shugaban Kwamitin Yaki da Rashawa a Majalisar Dattawa ke wakilta.

“An bayar da kwangilar ayyukan a kan naira miliyan 355, 391, 657. 95 tare da tsammanin za a kammala su bakidaya. Tawagar mu ta kunshi wakilan ICPC, kungiyoyin farar hula da ‘yan jarida wadanda duka za su bi diddigin ayyukan.”

“Hakan na da manufar gano ayyukan, yanayin ayyukan da adadin kudin da aka kashe a ayyukan da adadin kudin kwangila, ‘yan kwangila, kudaden da aka biya da gano mutanen da suka jagoranci ayyukan.” Ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

A cewarsa tawagar za ta kuma binciko kamfunan da suka yi ayyukan, binciken ko an cika sharuddan ayyukan da kudaden haraji. Ya ce za su duba kima da muhimmancin ayyukan ga al’ummar da aka yi domin su.

Ayyukan da za a gudanar da binciken gano su sun hada da samar da motoci a yankin Majalisar Dattawa a Sakkwato ta Gabas da Sanata Ibrahim Abdullahi Gobir ke wakilta da babura a Mazabar Sakkwato ta Arewa da Sanata Aliyu Wamakko, tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato ke wakilta.

Haka ma akwai binciken gano tabbatar da rarraba babura 188 a Mazabar Gwadabawa/Illela da Hon. Abdullahi Salame ke wakilta a Majalisar Wakilai.

Sauran sun hada da samar da takin zamani na NPK da fanfunan ruwa a Mazabar Kware/Wamakko da shirin karfafawa al’umma kan aikin gona a Mazabar Tarayya ta Bodinga/Dange/Shuni/Tureta wadda Hon. Balarabe Kakale ke wakilta a wa’adin zango na farko.

Tawagar ta riga ta ziyarci wasu daga cikin ayyukan da aka aiwatar a Mazabar Tarayya ta Sakkwato ta Arewa/Sakkwato ta Kudu da Bodinga/Dange/Shuni/Tureta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

Next Post

Gwamnatin APC Ta Yaudari ‘Yan Nijeriya – Kwankwaso

Related

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato
Tsaro

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

23 minutes ago
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

3 hours ago
Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025
Manyan Labarai

Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025

3 hours ago
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Jigila Kai Tsaye Zuwa Sin Da Indiya
Labarai

FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa

7 hours ago
Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya
Labarai

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

8 hours ago
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

9 hours ago
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Gwamnatin APC Ta Yaudari 'Yan Nijeriya - Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

June 16, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

June 16, 2025
Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025

Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025

June 16, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan

Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan

June 16, 2025
An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

June 16, 2025
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Jigila Kai Tsaye Zuwa Sin Da Indiya

FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa

June 16, 2025
Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

June 16, 2025
Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

June 16, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

June 16, 2025
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

June 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.