• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Ta Rufe Makarantu 68 Na Bogi A Nijeriya

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
ICPC Ta Rufe Makarantu 68 Na Bogi A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar da ke Yaki da Almundahana da Sauran Laifukan Cin Hanci (ICPC), ta ce ta rufe jami’o’i da kwalejin kimiyya da fasaha da ke bayar da shaidar digiri ta bogi 62 a fadin kasar.

Hukumar ta ce wannan abu ne da ke neman zama ruwan dare a Nijeriya, domin kuwa babu wata jiha a fadin kasar da ba a samu irin wannan makarantu ba a cikinta.

  • Dan Shekara Hudu Ya Kubuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Yobe
  • PDP Ta Zargi Makiyan Dimokuradiyya Da Kitsa Hargitsi A Gangamin Da Jam’iyyar Ta Yi A Kaduna

Cikin shekaru da ICPC ta kwashe tana gudanar da wani bincike a boye, ta kai ga gano adadin makarantu da suka hada da jami’o’i da kwaleji-kwaleji 62 na bogi da ke bayar da shaidar digiri a fadin Nijeriya.

Amma ta ce an fi samun irin wadannan makarantu a arewa ta tsakiyar Nijeriya.

ICPC ta ce ta bayyana wannan gagagrumar barna ne, domin shaida wa ‘yan Nijeriya cewa tana kallon duk wani mai shirin yin almundahana a kowane fanni.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Ta ce ko da za a dauke kai a ko ina, to ba dai a bangaren ilimi ba, domin kuwa duk kasar da ba ta da tsarin ilimi ingantacce, to gobenta za ta iya kasancewa cikin kila wa kala.

Muhammad Ashiru Baba shi ne shugaban sashen wayar da kan jama’a na ICPC, ya kuma ce abin takaici ne halin da ilimi ya tsinci kansa a Nijeriya.

Ya kara da cewa ”mafi yawan Jami’o’in ba su da ginin kansu, a maimakon haka suna amfani da gine-ginen Sakandire da na Furamaren da ba a karatu a karshen mako domin gudanar da karatunsu, kuma cikin shekara guda mutum zai samu shaidarsa”.

Wanda hakan ke nufin iyayen da suke kai yaransu irin wadannan wurare, sun kwana da sanin inda suke kai yaran nasu ba wajen kwarai ba ne.

Ashiru Baba ya ce a kwanakin baya har kama sansanin ‘yan bautar kasa suka yi na bogi, wani abu da suka jima yana daure musu kai.

ICPC ta cimma nasarar kulle wadannan jami’o’i ne ta hanyar bayanai da ta samu daga hukumar da ke kula da Jami’o’i ta kasa NUC, kuma tun daga 2016 ta ke gudanar da wannan aiki har ya zuwa yau.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ICPCIyayeJami'o'iKungiyar DalibaiKwalejojiMakarantun Bogi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mu Nemi Yafiyar ‘Yan Nijeriya Don Ba Lallai Mun Biya Musu Bukatunsu Ba – Aisha Buhari

Next Post

Zan Daukaka Kara Kan Hukuncin Kotu Da Ya Soke Takarata – Aisha Binani

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 hour ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

3 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

5 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

6 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

6 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

11 hours ago
Next Post
Zan Daukaka Kara Kan Hukuncin Kotu Da Ya Soke Takarata – Aisha Binani

Zan Daukaka Kara Kan Hukuncin Kotu Da Ya Soke Takarata - Aisha Binani

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.