• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illar Raba Kan Mata

by Bilkisu Tijjani
4 months ago
in Hannunka-Mai-Sanda
0
Illar Raba Kan Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zaman lafiya shi ne ginshikin duk wata rayuwa bama ace irin rayuwa ta iyali wadda idan aka yi sa a al’amura suna tafiya kamar yadda ya dace, shi kan shi ko su kansu masu irin wadannan halayen sai sun fi jin dadin rayuwar aure da matansu.Awai wani gidan da na sani ba fada mani aka yi ba,domin shi Maigidan abinda yake yi shi ne idan dan wancan matar ya isa ‘yaye sai ya kai ma kishiyarta ko abokiyar zama ta daya dakin.

Haka yake tafiyar da harkokin gidansa,wani yaron ma bai sanin mahaifiyarsa sai ranar daya kammala Jami’a, ko kammala yi ma kasa hidima abinda aka fi sani da Bautar kasa.Ita kuma ‘ya macen ba a nuna mata mahaifiyarta sai ranar da aka daura mata aure.

  • Ingancin Makarantu Masu Zaman Kansu Ya Tabarbare
  • Waiwayen Tsarin Hulda Da ƙasashen Waje Na Nijeriya A Matsayin Mafita

Yana kuma yin hakan ne domin ya samu hadin kan matan nasa wanda kuma haka abin ya kasance har bayan rayuwarsa.Zai kuma yi wuya ka shiga gida ka ji ana ta musanyar maganar da bata kamata ba tsakanin matansa.

Amma wasu Mazan ko Magidanta halayensu abin sai dai ayi sha’ani wai an cuci na kauye, da zarar sun yi wani sabon aure sai su canza yadda suke tafiyar da al’amuransu.Matar da Amarya ta tarar wato Uwargida sai a rika ci mata mutunci ta hanyar yin abubuwan da basu kamata ba, Wata rashin jituwa ko tashe- tashen hankula tsakanin matansu, sune suke kasancewar mafarin faruwar al’amarin.

Daga karshe dai wani har sai ya cimma burinsa na korar ita Uwargidan ta halayen shi daya canza, in aka samu wadda bata da hakuri koda kuwa ba sakinta yayi babata iya tsayawa da cigaba da ganin wulakanci.Bai ma tsayawa sai ta yi ma shi wani abinda bai dace ba tukuna hakanan sai ya dauki karan tsana ya rika nuna ta da shi. Babbar illar raba kan mata da wasu Magidanta suke yi ba karama bace wadda kuma take kawo matsalar da zata iya shafar rayuwar duk wadanda suke gidan baki daya. Domin kuwa matukar shi Maigidan da ya tara dukkan matanda suke gidan bai gyara halin sa na yin abubuwan da basu dace ba, don kawai ya farantawa ita Amaryar zuciyarta,to abin fa daga karshe ba zai haifar da da mai ido ba.Idan aka yi rashin sa’a har ita Uwragidan ta fita a sanadiyar ko shi Mijin ya sake ta,ko kuma taga cewar ba zata iya jure ma zaman gidan ba, a irin wannan yanayin ta yi tafiyarta.

Labarai Masu Nasaba

Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa

Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

A karo na farko matsalar da shi Maigidan zai fara fuskanta ko su ‘ya’yanta ita ce ta kula da tarbiyyarsu kamar yadda mahaifiyar su take yi masu,saboda ba dole bane kishoyinta ko kishiyarta su yi ma ‘ya’yan tarbiyyar yadda mahaifiyarsu take yi masu data dace.

Wannan ya nuna ke nan maganar gaskiyar ba ance wasu ba za su iya tarbiyyar ‘ya’yan wasu ba ne,amma abin kallo anan shi ne,wasu da biyu ne da gangan za su yi ta yi masu ingiza mai kantu ruwa suna sa su hanya ko hanyoyin da tarbiyarsu za ta gurvace wanda abin daga karshe su kasa rashin amfanar su kansu da ma masu hulda da su kai tsaye ko a kaikaice.

Shi ma mahaifin ko Maigidan da zai cigaba da aiwatar da irin yara tsanar ko kiyayyar da yake nunuwa nahaifiyar su ‘ya’yan zuwa gare su,duk wani abinda da suka yi ko dai dai ko akasin haka ba zai ce masu uffan ba, sais a masu idanu bama kamar idan aka yi rashin sa’a suna kanana.

Wannan ba karamar illa bace ta kan kuma faru a gidaje daban- daban sa salon halayen Maigida wanda ya kasance mai al’adarnan ta Auri–Saki. Saboda kuwa tana iya shafar al’ummar gidan gaba daya. Zaman lafiya da kwanciyar hankali ya kan yi wuya a ire-iren wadannan gidajen, ko Unguwa da ma Gari baki ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Waiwayen Tsarin Hulda Da ƙasashen Waje Na Nijeriya A Matsayin Mafita

Next Post

Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al’ummar Kano – Gwamna Abba

Related

Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa
Hannunka-Mai-Sanda

Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa

10 months ago
Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya
Hannunka-Mai-Sanda

Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

1 year ago
Next Post
Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al’ummar Kano – Gwamna Abba

Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al'ummar Kano - Gwamna Abba

LABARAI MASU NASABA

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.