ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illar Raba Kan Mata

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
Mata

Zaman lafiya shi ne ginshikin duk wata rayuwa bama ace irin rayuwa ta iyali wadda idan aka yi sa a al’amura suna tafiya kamar yadda ya dace, shi kan shi ko su kansu masu irin wadannan halayen sai sun fi jin dadin rayuwar aure da matansu.Awai wani gidan da na sani ba fada mani aka yi ba,domin shi Maigidan abinda yake yi shi ne idan dan wancan matar ya isa ‘yaye sai ya kai ma kishiyarta ko abokiyar zama ta daya dakin.

Haka yake tafiyar da harkokin gidansa,wani yaron ma bai sanin mahaifiyarsa sai ranar daya kammala Jami’a, ko kammala yi ma kasa hidima abinda aka fi sani da Bautar kasa.Ita kuma ‘ya macen ba a nuna mata mahaifiyarta sai ranar da aka daura mata aure.

  • Ingancin Makarantu Masu Zaman Kansu Ya Tabarbare
  • Waiwayen Tsarin Hulda Da ƙasashen Waje Na Nijeriya A Matsayin Mafita

Yana kuma yin hakan ne domin ya samu hadin kan matan nasa wanda kuma haka abin ya kasance har bayan rayuwarsa.Zai kuma yi wuya ka shiga gida ka ji ana ta musanyar maganar da bata kamata ba tsakanin matansa.

ADVERTISEMENT

Amma wasu Mazan ko Magidanta halayensu abin sai dai ayi sha’ani wai an cuci na kauye, da zarar sun yi wani sabon aure sai su canza yadda suke tafiyar da al’amuransu.Matar da Amarya ta tarar wato Uwargida sai a rika ci mata mutunci ta hanyar yin abubuwan da basu kamata ba, Wata rashin jituwa ko tashe- tashen hankula tsakanin matansu, sune suke kasancewar mafarin faruwar al’amarin.

Daga karshe dai wani har sai ya cimma burinsa na korar ita Uwargidan ta halayen shi daya canza, in aka samu wadda bata da hakuri koda kuwa ba sakinta yayi babata iya tsayawa da cigaba da ganin wulakanci.Bai ma tsayawa sai ta yi ma shi wani abinda bai dace ba tukuna hakanan sai ya dauki karan tsana ya rika nuna ta da shi. Babbar illar raba kan mata da wasu Magidanta suke yi ba karama bace wadda kuma take kawo matsalar da zata iya shafar rayuwar duk wadanda suke gidan baki daya. Domin kuwa matukar shi Maigidan da ya tara dukkan matanda suke gidan bai gyara halin sa na yin abubuwan da basu dace ba, don kawai ya farantawa ita Amaryar zuciyarta,to abin fa daga karshe ba zai haifar da da mai ido ba.Idan aka yi rashin sa’a har ita Uwragidan ta fita a sanadiyar ko shi Mijin ya sake ta,ko kuma taga cewar ba zata iya jure ma zaman gidan ba, a irin wannan yanayin ta yi tafiyarta.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa

A karo na farko matsalar da shi Maigidan zai fara fuskanta ko su ‘ya’yanta ita ce ta kula da tarbiyyarsu kamar yadda mahaifiyar su take yi masu,saboda ba dole bane kishoyinta ko kishiyarta su yi ma ‘ya’yan tarbiyyar yadda mahaifiyarsu take yi masu data dace.

Wannan ya nuna ke nan maganar gaskiyar ba ance wasu ba za su iya tarbiyyar ‘ya’yan wasu ba ne,amma abin kallo anan shi ne,wasu da biyu ne da gangan za su yi ta yi masu ingiza mai kantu ruwa suna sa su hanya ko hanyoyin da tarbiyarsu za ta gurvace wanda abin daga karshe su kasa rashin amfanar su kansu da ma masu hulda da su kai tsaye ko a kaikaice.

Shi ma mahaifin ko Maigidan da zai cigaba da aiwatar da irin yara tsanar ko kiyayyar da yake nunuwa nahaifiyar su ‘ya’yan zuwa gare su,duk wani abinda da suka yi ko dai dai ko akasin haka ba zai ce masu uffan ba, sais a masu idanu bama kamar idan aka yi rashin sa’a suna kanana.

Wannan ba karamar illa bace ta kan kuma faru a gidaje daban- daban sa salon halayen Maigida wanda ya kasance mai al’adarnan ta Auri–Saki. Saboda kuwa tana iya shafar al’ummar gidan gaba daya. Zaman lafiya da kwanciyar hankali ya kan yi wuya a ire-iren wadannan gidajen, ko Unguwa da ma Gari baki ɗaya.

Mata
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
Hannunka-Mai-Sanda

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

August 16, 2025
Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa
Hannunka-Mai-Sanda

Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa

July 8, 2024
Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya
Hannunka-Mai-Sanda

Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

December 30, 2023
Next Post
Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al’ummar Kano – Gwamna Abba

Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al'ummar Kano - Gwamna Abba

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.