ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illar Raba Kan Mata

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Mata

Zaman lafiya shi ne ginshikin duk wata rayuwa bama ace irin rayuwa ta iyali wadda idan aka yi sa a al’amura suna tafiya kamar yadda ya dace, shi kan shi ko su kansu masu irin wadannan halayen sai sun fi jin dadin rayuwar aure da matansu.Awai wani gidan da na sani ba fada mani aka yi ba,domin shi Maigidan abinda yake yi shi ne idan dan wancan matar ya isa ‘yaye sai ya kai ma kishiyarta ko abokiyar zama ta daya dakin.

Haka yake tafiyar da harkokin gidansa,wani yaron ma bai sanin mahaifiyarsa sai ranar daya kammala Jami’a, ko kammala yi ma kasa hidima abinda aka fi sani da Bautar kasa.Ita kuma ‘ya macen ba a nuna mata mahaifiyarta sai ranar da aka daura mata aure.

  • Ingancin Makarantu Masu Zaman Kansu Ya Tabarbare
  • Waiwayen Tsarin Hulda Da ƙasashen Waje Na Nijeriya A Matsayin Mafita

Yana kuma yin hakan ne domin ya samu hadin kan matan nasa wanda kuma haka abin ya kasance har bayan rayuwarsa.Zai kuma yi wuya ka shiga gida ka ji ana ta musanyar maganar da bata kamata ba tsakanin matansa.

ADVERTISEMENT

Amma wasu Mazan ko Magidanta halayensu abin sai dai ayi sha’ani wai an cuci na kauye, da zarar sun yi wani sabon aure sai su canza yadda suke tafiyar da al’amuransu.Matar da Amarya ta tarar wato Uwargida sai a rika ci mata mutunci ta hanyar yin abubuwan da basu kamata ba, Wata rashin jituwa ko tashe- tashen hankula tsakanin matansu, sune suke kasancewar mafarin faruwar al’amarin.

Daga karshe dai wani har sai ya cimma burinsa na korar ita Uwargidan ta halayen shi daya canza, in aka samu wadda bata da hakuri koda kuwa ba sakinta yayi babata iya tsayawa da cigaba da ganin wulakanci.Bai ma tsayawa sai ta yi ma shi wani abinda bai dace ba tukuna hakanan sai ya dauki karan tsana ya rika nuna ta da shi. Babbar illar raba kan mata da wasu Magidanta suke yi ba karama bace wadda kuma take kawo matsalar da zata iya shafar rayuwar duk wadanda suke gidan baki daya. Domin kuwa matukar shi Maigidan da ya tara dukkan matanda suke gidan bai gyara halin sa na yin abubuwan da basu dace ba, don kawai ya farantawa ita Amaryar zuciyarta,to abin fa daga karshe ba zai haifar da da mai ido ba.Idan aka yi rashin sa’a har ita Uwragidan ta fita a sanadiyar ko shi Mijin ya sake ta,ko kuma taga cewar ba zata iya jure ma zaman gidan ba, a irin wannan yanayin ta yi tafiyarta.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa

A karo na farko matsalar da shi Maigidan zai fara fuskanta ko su ‘ya’yanta ita ce ta kula da tarbiyyarsu kamar yadda mahaifiyar su take yi masu,saboda ba dole bane kishoyinta ko kishiyarta su yi ma ‘ya’yan tarbiyyar yadda mahaifiyarsu take yi masu data dace.

Wannan ya nuna ke nan maganar gaskiyar ba ance wasu ba za su iya tarbiyyar ‘ya’yan wasu ba ne,amma abin kallo anan shi ne,wasu da biyu ne da gangan za su yi ta yi masu ingiza mai kantu ruwa suna sa su hanya ko hanyoyin da tarbiyarsu za ta gurvace wanda abin daga karshe su kasa rashin amfanar su kansu da ma masu hulda da su kai tsaye ko a kaikaice.

Shi ma mahaifin ko Maigidan da zai cigaba da aiwatar da irin yara tsanar ko kiyayyar da yake nunuwa nahaifiyar su ‘ya’yan zuwa gare su,duk wani abinda da suka yi ko dai dai ko akasin haka ba zai ce masu uffan ba, sais a masu idanu bama kamar idan aka yi rashin sa’a suna kanana.

Wannan ba karamar illa bace ta kan kuma faru a gidaje daban- daban sa salon halayen Maigida wanda ya kasance mai al’adarnan ta Auri–Saki. Saboda kuwa tana iya shafar al’ummar gidan gaba daya. Zaman lafiya da kwanciyar hankali ya kan yi wuya a ire-iren wadannan gidajen, ko Unguwa da ma Gari baki ɗaya.

Mata
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Tuwon Alkama Da Miyar Taushe
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Kula Da Labba Domin Su Kasance Masu Laushi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Chicken Teriyaki Rice
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Kare Hannu Daga Bushewa

MASU ALAKA

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
Hannunka-Mai-Sanda

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

August 16, 2025
Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa
Hannunka-Mai-Sanda

Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa

July 8, 2024
Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya
Hannunka-Mai-Sanda

Tufka Da Warwarar Akidar Kwankwasiyya

December 30, 2023
Next Post
Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al’ummar Kano – Gwamna Abba

Ganduje Ya Haifar Da Babbar Matsala Ga Ci Gaban Al'ummar Kano - Gwamna Abba

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.