• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illolin Tsaka A Mahangar Addinin Musulunci —Dakta Jamil

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Illolin Tsaka A Mahangar Addinin Musulunci —Dakta Jamil
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

A yau muna tare da Sheikh Dakta Jamil Nasir Bebeji, Shugaban Cibiyar Bincike da Ba Da Magunguna Ta Addinin Musulunci ta Alyusrah Islamic Health Centre.

Kuma a wannan gabar za mu tattauna da shi akan wani abu da ya shige wa jama’a kai game da Tsaka, hakikaninta da irin abubuwan da ake ta jayayya akai na shin ko tana da cutarwa ga al’umma ko akasin haka. Kana za kuma mu ji hukuncinta kashe ta a shari’ance ta fuskar Hadisan manzon Allah, ingancinsu ko kuma akasin haka. Sannan kuma da irin nau’in cututtukan da dauke da su idan akwai in kuma babu duk dai za mu ji daga bakin Dakta

Dakta muna yi maka barka da shigowa wannan azure namu

Yawwa

Akwai hadisin Manzon Allah Sallallahu alaihi wasallam da ya yi umarni a kashe Tsaka, shin wannan Hadisi akwai shi, in akwai shi yaya ingancinsa yake?

A’uzu billahi misshaidanirrajim, min hamzihi wa nafyih, Bismillahirarrahmanirrahim. Wassalatu wassalamu ala man la Nabiyya ba’dahu. Assalamu alaikum warahmatullahi Ta’alah wabaratuhu. hadisai na game da Tsaka ingantattun hadisai ne, kuma in sha Allahu za mu fara karanto su mu ji su da kunnenmu. Na farko dai ita Tsaka dabba ce daga cikin halittun Allah Subhanahu Wata’ala wadanda ya halitta a bayan kasa, tun da muma mutane muna daga cikin halittun Allah Tabaraka Wata’alah, da aljanu gaba daya da mala’iku.

Hadisi na farko akwai hadisi da Imamu Bukhari ya ruwaito daga Nana Aisha Allah ya kara mata yarda, take cewa Manzon Allah Sallallahu ailihi wasallama ya yi magana game da Tsaka, sai ya ce mata “ Ita Tsaka tana daga cikin Fasikai, wato dabbobi fasikai, ka ga akwai dabbobi wadanda ko da masu cutarwa ne ba a sa su cikin fasikai ba. kamar zaki ka ga yana cutarwa in ka gan shi gudu za ka yi amma ba ya cikin fasikai. Akwai dabbobi biyar da aka sau a cikin fasikai duk da wasu suna saka har da su zakin tun da ai yana da fika, amma dalilai su kan kawo idan dalili ya juya a ya kan iya cin zaki, to zaki yana cikin wadanda aka yi kai-kawo a lamarinsa. Amma Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama Tsaka ya sanya cikin fasikai, wannan shi ne muhalisshahid.

Hadisi na ga wanda Imamu Muslim ya ruwaito, daga Sa’adu daga babansa, ya ce, Manzon Allah Ya yi umarnin a kashe Tsaka kuma ya sanya ta a cikin fasikai”. To Manzon Allah ya yi umarni da a kashe ta, shi kuwa umarnin manzon Allah ibada ne. akwai kuma hadisi da Imamu Bukhari ya ruwaita na Ummu Sharikin, Allah ya kara mata yarda, take cewa, Manzon Allah mai Tsida amincin Allah ya yi umarni da kashe Tsaka, ya ce, ta kasance ta yi busa a yayin da ake kokarin kona Annabi Ibrahim Alaihissalam bayan an jefa cikin wuta, wannan an kawo illa ce, wasu suna kawo shi a matsayin dalili a’a ba dalili bane illa ce, domin a lokacin da ake hada wutar domi a jefa shi duka dabbabi sun ki su ba da gudunmawa inda suka din kokarin su kashe wutar ma ita kuwa Tsaka ita kadai ce ta taimaka aka hura wutar.

To ka ga a nan labari kawai aka bayar na illolinta, cewa ita tsaka tana iya yi maka busa ta haifar maka da illa, wato daga suffofinta na illoli tana iya hura ka ta haifar maka da illa a jikinka. Kuma ba wai manzon Allah ya ce don waccan guda dayar ta yi wancan laifi shi ne zai sa ya ba da umarnin duk inda aka ga tsaka a kashe ta ba, a a ba haka bane. Sannan sai Hadisi da Imam Muslim ya fitar daga Aba Huraira, Allah ya kara yarda da shi yake cewa, Manzon llah Sallallahu alihi wasallama ya ce, Wanda ya kashe Tsaka a duka daya, yana da lada kaza da kaza, wato ana nufin duk wanda ya kashe ta a duka farko ladansa ya fi na ya kashe a duka na biyu haka ladan zai dinga raguwa, haka wanda ya kashe ta a duka na uku nan ma ladansa yana raguwa, wato ya danganta da dukan da ka yi mata, amma dai dukan farko in ka kashe ta ya fi lada. Kuma a gane dukkan Hadisan nan fa ingantattu ne daga Bukhari sai Muslim.

To ka ga wannan Hadisin yana karfafar kashe ta, yana nufin in ka kashe ta da niyyar koyi da manzon Allah lada fa za ka samu, misali ai an ce mu kashe duk abin da zai cutar da mu kamar sauro ai ka ga suna cutarwa kuma an ce mu kashe su amma me ya sa ba a ce in ka kshe su kana da lada ba, amma ka kashe su kuma yana da kyau domin zai maka illa. Amma ita wannan Tsaka lada za ka samu, na farko kenan, na biyu kuma yana da muhimmancin ka yi mata bugu da karfi ka kashe ka kwashe ta ka je ka jefar. Sannan kuma hikima ta uku, wannan Hadisin da ya zo wannan sigar kenan wanda ya yi mata bugu na hudu ma za a bashi lada amma bai kai wanda ya yi mata bugu na farko ba, har zuwa goma. To wani hadisi da Imam Muslim ya fitar.

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce, wanda ya kashe Tsaka a duka daya za a rubuta masa lada dari, idan kuma ka yi mata dukan da wuce daya sannan ta mutu to za a baka ladan da bai kai wannan ba. ita Tsaka a duk dabbobin da suke ta’ammali a cikin mutane babu dabbar da shaidanu suka amfani da ita kamar ita wato aljanu, suna yawan yin amfani da ita wajen yin abubuwa da yawa, shi ya sa take yin sanadin mutuwar mutane sosai. To wannan ka ga hadisai ingantattu wadanda ingancinsu ya bayyana kamar hasken ran aba maganar wani kokwanto a kansu cewa Tsaka in an ganta a kashe ta.

To Dakta tambayarmu ta biyu ita ce, akwai wata likita da aka tattauna da ita, inda ta nuna cewa, ita Tsaka ba ta da wata illa, idan ma tana da wata matsala bai wuce irin cututtukan sauran kwari suke haifarwa ba, kamar su cutar Typod da sauransu, amma ta ce ba ta dauke da guba kamar A yau muna tare da Sheikh Dakta Jamil Nasir Bebeji, Shugaban Cibiyar Bincike da Ba Da Magunguna Ta Addinin Musulunci ta Alyusrah Islamic Health Centre.

Kuma a wannan gabar za mu tattauna da shi akan wani abu da ya shige wa jama’a kai game da Tsaka, hakikaninta da irin abubuwan da ake ta jayayya akai na shin ko tana da cutarwa ga al’umma ko akasin haka. Kana za kuma mu ji hukuncinta kashe ta a shari’ance ta fuskar Hadisan manzon Allah, ingancinsu ko kuma akasin haka. Sannan kuma da irin nau’in cututtukan da dauke da su idan akwai in kuma babu duk dai za mu ji daga bakin Dakta

Dakta muna yi maka barka da shigowa wannan azure namu

Yawwa

Akwai hadisin Manzon Allah Sallallahu alaihi wasallam da ya yi umarni a kashe Tsaka, shin wannan Hadisi akwai shi, in akwai shi yaya ingancinsa yake?

A’uzu billahi misshaidanirrajim, min hamzihi wa nafyih, Bismillahirarrahmanirrahim. Wassalatu wassalamu ala man la Nabiyya ba’dahu. Assalamu alaikum warahmatullahi Ta’alah wabaratuhu. hadisai na game da Tsaka ingantattun hadisai ne, kuma in sha Allahu za mu fara karanto su mu ji su da kunnenmu. Na farko dai ita Tsaka dabba ce daga cikin halittun Allah Subhanahu Wata’ala wadanda ya halitta a bayan kasa, tun da muma mutane muna daga cikin halittun Allah Tabaraka Wata’alah, da aljanu gaba daya da mala’iku.  Hadisi na farko akwai hadisi da Imamu Bukhari ya ruwaito daga Nana Aisha Allah ya kara mata yarda, take cewa Manzon Allah Sallallahu ailihi wasallama ya yi magana game da Tsaka, sai ya ce mata “ Ita Tsaka tana daga cikin Fasikai, wato dabbobi fasikai, ka ga akwai dabbobi wadanda ko da masu cutarwa ne ba a sa su cikin fasikai ba. kamar zaki ka ga yana cutarwa in ka gan shi gudu za ka yi amma ba ya cikin fasikai. Akwai dabbobi biyar da aka sau a cikin fasikai duk da wasu suna saka har da su zakin tun da ai yana da fika, amma dalilai su kan kawo idan dalili ya juya a ya kan iya cin zaki, to zaki yana cikin wadanda aka yi kai-kawo a lamarinsa. Amma Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama Tsaka ya sanya cikin fasikai, wannan shi ne muhalisshahid. Hadisi na ga wanda Imamu Muslim ya ruwaito, daga Sa’adu daga babansa, ya ce, Manzon Allah Ya yi umarnin a kashe Tsaka kuma ya sanya ta a cikin fasikai”. To Manzon Allah ya yi umarni da a kashe ta, shi kuwa umarnin manzon Allah ibada ne. akwai kuma hadisi da Imamu Bukhari ya ruwaita na Ummu Sharikin, Allah ya kara mata yarda, take cewa, Manzon Allah mai Tsida amincin Allah ya yi umarni da kashe Tsaka, ya ce, ta kasance ta yi busa a yayin da ake kokarin kona Annabi Ibrahim Alaihissalam bayan an jefa cikin wuta, wannan an kawo illa ce, wasu suna kawo shi a matsayin dalili a’a ba dalili bane illa ce, domin a lokacin da ake hada wutar domi a jefa shi duka dabbabi sun ki su ba da gudunmawa inda suka din kokarin su kashe wutar ma ita kuwa Tsaka ita kadai ce ta taimaka aka hura wutar. To ka ga a nan labari kawai aka bayar na illolinta, cewa ita tsaka tana iya yi maka busa ta haifar maka da illa, wato daga suffofinta na illoli tana iya hura ka ta haifar maka da illa a jikinka. Kuma ba wai manzon Allah ya ce don waccan guda dayar ta yi wancan laifi shi ne zai sa ya ba da umarnin duk inda aka ga tsaka a kashe ta ba, a a ba haka bane. Sannan sai Hadisi da Imam Muslim ya fitar daga Aba Huraira, Allah ya kara yarda da shi yake cewa, Manzon llah Sallallahu alihi wasallama ya ce, Wanda ya kashe Tsaka a duka daya, yana da lada kaza da kaza, wato ana nufin duk wanda ya kashe ta a duka farko ladansa ya fi na ya kashe a duka na biyu haka ladan zai dinga raguwa, haka wanda ya kashe ta a duka na uku nan ma ladansa yana raguwa, wato ya danganta da dukan da ka yi mata, amma dai dukan farko in ka kashe ta ya fi lada. Kuma a gane dukkan Hadisan nan fa ingantattu ne daga Bukhari sai Muslim. To ka ga wannan Hadisin yana karfafar kashe ta, yana nufin in ka kashe ta da niyyar koyi da manzon Allah lada fa za ka samu, misali ai an ce mu kashe duk abin da zai cutar da mu kamar sauro ai ka ga suna cutarwa kuma an ce mu kashe su amma me ya sa ba a ce in ka kshe su kana da lada ba, amma ka kashe su kuma yana da kyau domin zai maka illa. Amma ita wannan Tsaka lada za ka samu, na farko kenan, na biyu kuma yana da muhimmancin ka yi mata bugu da karfi ka kashe ka kwashe ta ka je ka jefar. Sannan kuma hikima ta uku, wannan Hadisin da ya zo wannan sigar kenan wanda ya yi mata bugu na hudu ma za a bashi lada amma bai kai wanda ya yi mata bugu na farko ba, har zuwa goma. To wani hadisi da Imam Muslim ya fitar. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce, wanda ya kashe Tsaka a duka daya za a rubuta masa lada dari, idan kuma ka yi mata dukan da wuce daya sannan ta mutu to za a baka ladan da bai kai wannan ba. ita Tsaka a duk dabbobin da suke ta’ammali a cikin mutane babu dabbar da shaidanu suka amfani da ita kamar ita wato aljanu, suna yawan yin amfani da ita wajen yin abubuwa da yawa, shi ya sa take yin sanadin mutuwar mutane sosai. To wannan ka ga hadisai ingantattu wadanda ingancinsu ya bayyana kamar hasken ran aba maganar wani kokwanto a kansu cewa Tsaka in an ganta a kashe ta.

To Dakta tambayarmu ta biyu ita ce, akwai wata likita da aka tattauna da ita, inda ta nuna cewa, ita Tsaka ba ta da wata illa, idan ma tana da wata matsala bai wuce irin cututtukan sauran kwari suke haifarwa ba, kamar su cutar Typod da sauransu, amma ta ce ba ta dauke da guba kamar yadda mutane ke fada, yaya lamarin yake. Shin akwai wani tawili da za a yi a kan wannan magana tata, misalin kamar ita ta yi magana ce a bincikenta na ilimin zamani, shin yaya abin yake a ilimin likitanci na Musulunci tun da shi Musulunci wayayyen addini ne?

Lallai na dan so in ji wannan maganar, kuma bayan na ji maganar an yi min wannan tambayar kafin ku ku yi min tambayar na dan bibiyi bayanan nata, sunanta Zainab Abubakar, wacce ita likitar dabbobi ce da take zaune a wani asibiti a nan Nyanya. Abin da ta yi bayani a kai akwai gaskiya akwai kuma rashin gaskiya, amma dadin da na ji shi ne, bayanan nata sun tabbatar da Hadisan Manzon Allah Sallallahu alaihi wasallam, ta yi bayanai kuma bayanan su suka karfafa duk abin da muka karanta a wannan hadisi, kenan manzon Allah ba da ka ya fada ya ce a kashe ta ba, tun da a bayananta ta ce Tsakar nan tana saurin dauko cututtuka sai ta hau kan abincin mutane sai a zo a kamu da cututtuka duk har da Typod. Sannan kuma ta ce ta kan saka yawunta ko kuma fitsarinta akan wasu abubuwa idan aka zo aka taba sai a kamu da cututtuka, to ka ga wannan ta tabbatar da cewa ba wai son zuciyarsa ne ya sa ya fada cewa a kashe din ba. ta saukaka mana wahalar duk wasu ma bayanai na illilin ita wannan tsakar. To amma inda ta fadi cewa din nan wato ita Tsakar a karankanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AddiniTsaka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sake Dawowar Matsalar Tsaro

Next Post

Yadda Ake Fahimtar Ma’anar Alfahari Da Al’adun Kasar Sin Daga Dakin Ibadar Three-Su

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

6 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

12 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

17 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

21 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

22 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

2 days ago
Next Post
Yadda Ake Fahimtar Ma’anar Alfahari Da Al’adun Kasar Sin Daga Dakin Ibadar Three-Su

Yadda Ake Fahimtar Ma’anar Alfahari Da Al’adun Kasar Sin Daga Dakin Ibadar Three-Su

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.