• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IMMOWA Ta Horar Da Mata Da Yaran Jami’an Shige Da Fice Sana’o’i  

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
IMMOWA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar matan jami’an hukumar shige da fice ta ƙasa (IMMOWA) ta horar da mata da yara sana’o’in dogaro da kai.

Ƙungiyar ta yi bikin bai wa waɗanda suka samu horon takardun shaida a shalkwatan hukumar ta NIS da ke Abuja.

  • An Kama Mai Shiga Tsakanin Iyalai Da Masu Garkuwar Jirgin Kasan Kaduna A Masar

Da take gabatar da jawabi lokacin bikin, Uwargidan shugaban hukumar shige da fita ta ƙasa, Hajiya Maryam Isah Jere ta nuna jin daɗinta bisa samun nasarar horar da mata da yara sana’o’in dogaro da kai tare da ɗora yara a tafarkin tarbiya.

Shugabar ƙungiyar ta ja kunnen waɗanda suka amfana da shirin da su yi amfani da abubuwan da suka koya wajen tallafa wa kansu da kuma al’umma gaba ɗaya.

“Ina ƙara wa waɗanda suka amfana da wannan horo ƙwarin gwiwa da su ci gaba da gudanar da sana’o’in da suka koya wajen inganta rayuwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

“Haka kuma ina jinjina ga dukkan waɗanda suka taimaka har aka samu nasarar gudanar da wannan horo. Wannan shirin yana bunƙasa ƙungiyar IMMOWA, wanda yake samun tallafi daga wurin maigidana da sauran jami’ai da ke ƙoƙarin bunƙasa rayuwar mata da yara,” in ji Hajiya Maryam.

Shugabar IMMOWA ta ƙara da cewa maƙasudin wannan shirin shi ne, saboda rashin tsaro da ake fama da shi wanda ya sa yara suna zaune a gida lokacin da iyayansu suke wuraren aiki. Ta ce sun yi tunanin haɗa yaran wuri ɗaya lokacin da iyayensu suke ofis, domin su koyi sana’o’in dogaro da kai.

A cewarta, ta gamsu da irin sakamakon da shirin ya bayar, domin tana ɗaya daga cikin waɗanda suke halartar horon a ko da yaushe tare da mambobin ƙugiyar IMMOWA.

Ta ce wasu daga cikin iyayen yaran suna kiran ta a waya domin nuna godiya da irin tarbiyar da yaran suka samu, inda suka ce a baya yaran ba sa iya gaida kansu, amma a yanzu suna yi. “Sai dai kuma ni ba na buƙatar godiyar mutane, ina neman lada daga wurin Allah.”

Shi ma da yake jawabi, Shugaban hukumar NIS, Isah Idris Jere ya bayyana cewa shirin ƙungiyar IMMOWA ya zo a kan gaɓa ta yadda zai bunƙasa rayuwar jami’ai mata da yaransu.

Wanda ɗaya daga cikin manyan mataimakansa, DCG Dupe Anyalechi ta wakilta a taron, CGI Isah Jere ya ce ƙungiyar ta sauya akalar matan jami’an hukumar ta yadda za su taimaka wa iyalansu da kuma al’umma gaba ɗaya daga abin da suka koya.

Ƙungiyar ta horar da mata da yara yadda ake haɗa sabulu da jaka da burodi da kek da dai sauran kayayyaki da ake amfani da su na yau da kullun.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Zababben Shugaban Kenya

Next Post

NIS Da NDLEA Reshen Bayelsa Sun Yi Ƙawancen Fatattakar Miyagun Ƙwayoyi Da Baƙin Haure

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

3 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

6 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

16 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

18 hours ago
Next Post
NDLEA

NIS Da NDLEA Reshen Bayelsa Sun Yi Ƙawancen Fatattakar Miyagun Ƙwayoyi Da Baƙin Haure

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.