• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IMMOWA Ta Horar Da Mata Da Yaran Jami’an Shige Da Fice Sana’o’i  

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
IMMOWA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar matan jami’an hukumar shige da fice ta ƙasa (IMMOWA) ta horar da mata da yara sana’o’in dogaro da kai.

Ƙungiyar ta yi bikin bai wa waɗanda suka samu horon takardun shaida a shalkwatan hukumar ta NIS da ke Abuja.

  • An Kama Mai Shiga Tsakanin Iyalai Da Masu Garkuwar Jirgin Kasan Kaduna A Masar

Da take gabatar da jawabi lokacin bikin, Uwargidan shugaban hukumar shige da fita ta ƙasa, Hajiya Maryam Isah Jere ta nuna jin daɗinta bisa samun nasarar horar da mata da yara sana’o’in dogaro da kai tare da ɗora yara a tafarkin tarbiya.

Shugabar ƙungiyar ta ja kunnen waɗanda suka amfana da shirin da su yi amfani da abubuwan da suka koya wajen tallafa wa kansu da kuma al’umma gaba ɗaya.

“Ina ƙara wa waɗanda suka amfana da wannan horo ƙwarin gwiwa da su ci gaba da gudanar da sana’o’in da suka koya wajen inganta rayuwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

“Haka kuma ina jinjina ga dukkan waɗanda suka taimaka har aka samu nasarar gudanar da wannan horo. Wannan shirin yana bunƙasa ƙungiyar IMMOWA, wanda yake samun tallafi daga wurin maigidana da sauran jami’ai da ke ƙoƙarin bunƙasa rayuwar mata da yara,” in ji Hajiya Maryam.

Shugabar IMMOWA ta ƙara da cewa maƙasudin wannan shirin shi ne, saboda rashin tsaro da ake fama da shi wanda ya sa yara suna zaune a gida lokacin da iyayansu suke wuraren aiki. Ta ce sun yi tunanin haɗa yaran wuri ɗaya lokacin da iyayensu suke ofis, domin su koyi sana’o’in dogaro da kai.

A cewarta, ta gamsu da irin sakamakon da shirin ya bayar, domin tana ɗaya daga cikin waɗanda suke halartar horon a ko da yaushe tare da mambobin ƙugiyar IMMOWA.

Ta ce wasu daga cikin iyayen yaran suna kiran ta a waya domin nuna godiya da irin tarbiyar da yaran suka samu, inda suka ce a baya yaran ba sa iya gaida kansu, amma a yanzu suna yi. “Sai dai kuma ni ba na buƙatar godiyar mutane, ina neman lada daga wurin Allah.”

Shi ma da yake jawabi, Shugaban hukumar NIS, Isah Idris Jere ya bayyana cewa shirin ƙungiyar IMMOWA ya zo a kan gaɓa ta yadda zai bunƙasa rayuwar jami’ai mata da yaransu.

Wanda ɗaya daga cikin manyan mataimakansa, DCG Dupe Anyalechi ta wakilta a taron, CGI Isah Jere ya ce ƙungiyar ta sauya akalar matan jami’an hukumar ta yadda za su taimaka wa iyalansu da kuma al’umma gaba ɗaya daga abin da suka koya.

Ƙungiyar ta horar da mata da yara yadda ake haɗa sabulu da jaka da burodi da kek da dai sauran kayayyaki da ake amfani da su na yau da kullun.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Zababben Shugaban Kenya

Next Post

NIS Da NDLEA Reshen Bayelsa Sun Yi Ƙawancen Fatattakar Miyagun Ƙwayoyi Da Baƙin Haure

Related

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

8 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

10 hours ago
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Labarai

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

11 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

12 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

13 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

16 hours ago
Next Post
NDLEA

NIS Da NDLEA Reshen Bayelsa Sun Yi Ƙawancen Fatattakar Miyagun Ƙwayoyi Da Baƙin Haure

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.