ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IMMOWA Ta Horar Da Mata Da Yaran Jami’an Shige Da Fice Sana’o’i  

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
IMMOWA

Ƙungiyar matan jami’an hukumar shige da fice ta ƙasa (IMMOWA) ta horar da mata da yara sana’o’in dogaro da kai.

Ƙungiyar ta yi bikin bai wa waɗanda suka samu horon takardun shaida a shalkwatan hukumar ta NIS da ke Abuja.

  • An Kama Mai Shiga Tsakanin Iyalai Da Masu Garkuwar Jirgin Kasan Kaduna A Masar

Da take gabatar da jawabi lokacin bikin, Uwargidan shugaban hukumar shige da fita ta ƙasa, Hajiya Maryam Isah Jere ta nuna jin daɗinta bisa samun nasarar horar da mata da yara sana’o’in dogaro da kai tare da ɗora yara a tafarkin tarbiya.

ADVERTISEMENT

Shugabar ƙungiyar ta ja kunnen waɗanda suka amfana da shirin da su yi amfani da abubuwan da suka koya wajen tallafa wa kansu da kuma al’umma gaba ɗaya.

“Ina ƙara wa waɗanda suka amfana da wannan horo ƙwarin gwiwa da su ci gaba da gudanar da sana’o’in da suka koya wajen inganta rayuwarsu.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

“Haka kuma ina jinjina ga dukkan waɗanda suka taimaka har aka samu nasarar gudanar da wannan horo. Wannan shirin yana bunƙasa ƙungiyar IMMOWA, wanda yake samun tallafi daga wurin maigidana da sauran jami’ai da ke ƙoƙarin bunƙasa rayuwar mata da yara,” in ji Hajiya Maryam.

Shugabar IMMOWA ta ƙara da cewa maƙasudin wannan shirin shi ne, saboda rashin tsaro da ake fama da shi wanda ya sa yara suna zaune a gida lokacin da iyayansu suke wuraren aiki. Ta ce sun yi tunanin haɗa yaran wuri ɗaya lokacin da iyayensu suke ofis, domin su koyi sana’o’in dogaro da kai.

A cewarta, ta gamsu da irin sakamakon da shirin ya bayar, domin tana ɗaya daga cikin waɗanda suke halartar horon a ko da yaushe tare da mambobin ƙugiyar IMMOWA.

Ta ce wasu daga cikin iyayen yaran suna kiran ta a waya domin nuna godiya da irin tarbiyar da yaran suka samu, inda suka ce a baya yaran ba sa iya gaida kansu, amma a yanzu suna yi. “Sai dai kuma ni ba na buƙatar godiyar mutane, ina neman lada daga wurin Allah.”

Shi ma da yake jawabi, Shugaban hukumar NIS, Isah Idris Jere ya bayyana cewa shirin ƙungiyar IMMOWA ya zo a kan gaɓa ta yadda zai bunƙasa rayuwar jami’ai mata da yaransu.

Wanda ɗaya daga cikin manyan mataimakansa, DCG Dupe Anyalechi ta wakilta a taron, CGI Isah Jere ya ce ƙungiyar ta sauya akalar matan jami’an hukumar ta yadda za su taimaka wa iyalansu da kuma al’umma gaba ɗaya daga abin da suka koya.

Ƙungiyar ta horar da mata da yara yadda ake haɗa sabulu da jaka da burodi da kek da dai sauran kayayyaki da ake amfani da su na yau da kullun.

 

IMMOWA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
NDLEA

NIS Da NDLEA Reshen Bayelsa Sun Yi Ƙawancen Fatattakar Miyagun Ƙwayoyi Da Baƙin Haure

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.