• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2023 a jam’iyyar APC, Sadique Baba Abubakar, ya nuna kwarin guiwar cewa zai samu nasarar a kotun sauraren kararrakin zabe.

Abubakar ya ce a zaben da aka gudanar shi ne ya samu nasara kuma yana da tulin hujjojin da za su gabatar a gaban kotun sauraron kararrakin zabe da hakan zai kai a dawo masa da wadanda suka zabe shi kujerar.

  • Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi
  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji

A hirarsa da ‘yan jarida bayan dawowarsa daga tafiya a ranar Litinin a Bauchi, Sadique ya ce, sashin shari’a a kasar nan yanzu ya ingantu don haka yana da cikakken kwarin guiwar za su wanzar da adalci da gaskiya a tsakani.

“Nasara a hannun Allah ya ke. Mun tabbatar zalumci aka yi kuma da izinin Allah, Allah zai kwato hakkin jama’a. Sannan mun tabbatar yanayin shari’a na Nijeriya na da kyau don mutane ne adilai wadanda za su tabbatar da gaskiya.”

A cewarsa, “Muna godiya wa Allah (SWT) wanda ya ba mu dama muka dawo bayan mun fara wannan gwagwarmayar da muka sanya a gaba na tabbatar da cewa an kwato hakkin jama’a an maida musu.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

“Wannan gwagwarmayar mun dauke shi kuma da izinin Allah, Allah zai ba mu nasara a kai.”

Ya gode wa jama’a bisa addu’o’in da ya ce sun yi masa musamman a lokacin azumi da kuma fatan alkairi da suke masa, kana ya kuma jinjina wa kokarin jam’iyyar APC da ta yi kuma take musu. Sai ya nemi masoya da magoya bayansa da su cigaba da kasance masu bin doka da oda har zuwa lokacin da kotu za ya saurari kararsa.

Abubakar ya tabbatar da cewa za su ci gaba da neman hakkinsu babu dare ko rana jar sai sun tabbatar sun kwace mulki, “Ina da kwarin guiwar Allah zai kwato wa jama’a hakkinsu domin Allah ya san abun da ya faru a lokacin zaben nan kuma mun tabbatar matakan da muka dauka za su fito da abubuwan da ake nema na ganin an kwato hakkin jama’a an dawo da shi.

“Na tabbatar da jama’anmu ba su bukatar cigaba da tsarin da ba a biyan albashi, tsarin da yara ke karatu a kasa alhalin ana nan ana gina manya-manyan ofisoshi na biliyoyi wanda ba shi ne ya dami al’umma ba.

“Saboda haka ganin yadda mutane suka ba mu hadin kai a ziyarar da muka kai kananan hukumomi muka ga ya wajaba a kanmu mu cigaba da wannan gwagwarmayar har sai mun tabbatar an kwato hakkin jama’a.”

Idan za ku tuna dai a zaben da aka fafata na 2023 da jam’iyyun siyasa daban-daban guda 14 suka shiga aka fafata da su, sakamakon ya nuna cewa Gwamnan da ke kan kujerar Bala Muhammad na jam’iyyar PDP ya samu nasarar tazarce da kuri’u 525, 280 yayin da abokin hamayyarsa na kusa-kusa Sadique Baba Abubakar ya tashi da kuri’u 432, 272 kamar yadda INEC ta shelanta. To sai dai Abubakar ya kalubanci sakamakon a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version