• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Dalilin Da Ya Sa Amurka Ta Hura Wutar Rikici Game Da “Yin Takara A Sararin Samaniya” Tare Da Kasar Sin A Argentina?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ina Dalilin Da Ya Sa Amurka Ta Hura Wutar Rikici Game Da “Yin Takara A Sararin Samaniya” Tare Da Kasar Sin A Argentina?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar kula da sararin samaniya ta kasar Amurka Bill Nelson, ya ziyarci kasar Argentina a ranar 27 ga watan nan, inda a wajen wani taron manema labarai da aka yi a birnin Buenos Aires, Nelson ya ayyana nasarorin da kasar Sin ta samu wajen binciken duniyar wata, da duniyar Mars, tare da bayyana cewa, a halin yanzu Sin da Amurka suna yin takara kan harkokin sararin samaniya.

Wannan ba shi ne karon farko da manyan jami’an Amurka, suke hura wutar rikici kan batun sararin samaniya a kasar Argentina ba. A watan Maris din shekara ta 2022 ma, kwamandar rundunar sojojin Amurka dake kudancin kasar wato USSOUTHCOM, Laura Richardson, ta ziyarci Argentina, inda ta ce tashar binciken sararin samaniya mai nisa ta hadin-gwiwar Sin da Argentina dake jihar Neuquén, tasha ce ta aikin soja.

  • Yadda Al’adu Nagari Ke Rainon Sinawa: Tarihi Daga Cibiyar Yinxu Ta Anyang Dake Kara Fahimtar Da Sirrin Wayewar Kan Sinawa

To sai dai a nasa bangare, ministan kula da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha na Argentina Daniel Filmus, ya maida martani kan wannan furuci na Laura, inda ya ce, kasarsa na amfani da tashar dake jihar Neuquén don gudanar da hadin-gwiwa tare da kasar Sin ne a fannin binciken sararin samaniya da taurarin dan Adam, kamar yadda kasar take yi da kasashen Turai.

Hakikanin gaskiya, tun a shekara ta 2012, hukumar kula da harkokin sararin samaniya ta Turai, ta kafa tashar binciken sararin samaniya mai nisa a Argentina, amma ko me ya sa Amurka ke zargin kasar Sin ita kadai?

Tun dai lokacin fara binciken harkokin sararin samaniya ya zuwa yanzu, kasar Sin na tsayawa kan fannin zaman lafiya. Kamar tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin da a yanzu haka take aiki a sararin samaniyar, wadda aka bude ga dukkan kasashe membobin Majalisar Dinkin Duniya, wanda hakan ya zama karon farko a tarihi na yin hakan. Wannan ya shaida niyyar kasar Sin na binciken sararin samaniya, wanda ba za’a iya shafa mata bakin fenti kan sa ba.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Sararin samaniya, gida ne ga daukacin al’ummar duniya, ba wai wuri ne da wata kasa ke iya nuna fin karfinta ba. Kaza lika bai kamata wasu Amurkawa, su rike tsoffin ra’ayoyinsu na da ba, kuma bai kamata a maimaita ayyukan lokacin yakin cacar baka ba, wannan ba zai yiwu ba. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna

Next Post

Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

4 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

6 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

6 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

7 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

8 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

10 hours ago
Next Post
Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.