ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Dalilin Da Ya Sa Amurka Ta Hura Wutar Rikici Game Da “Yin Takara A Sararin Samaniya” Tare Da Kasar Sin A Argentina?

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Shugaban hukumar kula da sararin samaniya ta kasar Amurka Bill Nelson, ya ziyarci kasar Argentina a ranar 27 ga watan nan, inda a wajen wani taron manema labarai da aka yi a birnin Buenos Aires, Nelson ya ayyana nasarorin da kasar Sin ta samu wajen binciken duniyar wata, da duniyar Mars, tare da bayyana cewa, a halin yanzu Sin da Amurka suna yin takara kan harkokin sararin samaniya.

Wannan ba shi ne karon farko da manyan jami’an Amurka, suke hura wutar rikici kan batun sararin samaniya a kasar Argentina ba. A watan Maris din shekara ta 2022 ma, kwamandar rundunar sojojin Amurka dake kudancin kasar wato USSOUTHCOM, Laura Richardson, ta ziyarci Argentina, inda ta ce tashar binciken sararin samaniya mai nisa ta hadin-gwiwar Sin da Argentina dake jihar Neuquén, tasha ce ta aikin soja.

  • Yadda Al’adu Nagari Ke Rainon Sinawa: Tarihi Daga Cibiyar Yinxu Ta Anyang Dake Kara Fahimtar Da Sirrin Wayewar Kan Sinawa

To sai dai a nasa bangare, ministan kula da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha na Argentina Daniel Filmus, ya maida martani kan wannan furuci na Laura, inda ya ce, kasarsa na amfani da tashar dake jihar Neuquén don gudanar da hadin-gwiwa tare da kasar Sin ne a fannin binciken sararin samaniya da taurarin dan Adam, kamar yadda kasar take yi da kasashen Turai.

ADVERTISEMENT

Hakikanin gaskiya, tun a shekara ta 2012, hukumar kula da harkokin sararin samaniya ta Turai, ta kafa tashar binciken sararin samaniya mai nisa a Argentina, amma ko me ya sa Amurka ke zargin kasar Sin ita kadai?

Tun dai lokacin fara binciken harkokin sararin samaniya ya zuwa yanzu, kasar Sin na tsayawa kan fannin zaman lafiya. Kamar tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin da a yanzu haka take aiki a sararin samaniyar, wadda aka bude ga dukkan kasashe membobin Majalisar Dinkin Duniya, wanda hakan ya zama karon farko a tarihi na yin hakan. Wannan ya shaida niyyar kasar Sin na binciken sararin samaniya, wanda ba za’a iya shafa mata bakin fenti kan sa ba.

LABARAI MASU NASABA

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Sararin samaniya, gida ne ga daukacin al’ummar duniya, ba wai wuri ne da wata kasa ke iya nuna fin karfinta ba. Kaza lika bai kamata wasu Amurkawa, su rike tsoffin ra’ayoyinsu na da ba, kuma bai kamata a maimaita ayyukan lokacin yakin cacar baka ba, wannan ba zai yiwu ba. (Murtala Zhang)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela
Daga Birnin Sin

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
Daga Birnin Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
Daga Birnin Sin

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Next Post
Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.