• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

by Abba Ibrahim Wada
4 hours ago
in Wasanni
0
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan uwan shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa Jude Bellingham wanda ke taka leda a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid Jobe Bellingham ya nuna sha’awar samun ɗaukaka kwatankwacin yadda ɗan uwan nasa ya samu a fagen ƙwallon ƙafa, wannan buri nasa ya fara cika tun ba’yan komawa Borrusia Dortmund inda Jude Bellingham ɗin ya taka leda kafin ya tafi Madrid a bazara.

Shekaru biyu ne kacal tsakanin Jude mai shekaru 21 da Jobe mai shekaru 19, Jude Bellingham ya koma Real Madrid a shekarar 2023 ba’yan shekaru uku a Dortmund, ɗan wasan tsakiyar na tawagar Ingila, Jude ya zama ɗaya daga cikin mafi kyawun ‘yan wasa a duniya a cikin ‘‘yan shekarun nan, Bellingham ƙarami ya koma Dortmund ne a watan Yuni daga Sunderland duk da cewa sun samu tikitin buga gasar Firimiya ta bana.

  • Majalisar Wakilai Ta Amince Da Kudiri 120 Cikin Wata Shida – Hon. Tajudeen
  • Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

“Ina da wannan burin a cikin rayuwata sannan kuma ina da dama domin har ‘yanzu ni matashi ne” Bellingham ya shaida wa manema labarai a sansanin shirye-shiryen kakar wasa na Dortmund dake Austria, ya ƙara da cewa “Wannan shawara ta zuwa Dortmund shawara ce da na ‘yanke ta ƙashin kaina wadda ba kowane zai fahimta ba”.

Bellingham ya fara buga wasansa na farko a Dortmund a gasar cin kofin duniya na ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa da aka kammala a ƙasar Amurka, inda ya zura ƙwallo ɗaya kuma ya taimaka aka ci ɗaya a wasanni huɗu da ya buga, kamar yadda ya yi a Sunderland, ƙaramin Bellingham ‘yana sanya sunansa na farko Jobe a ba’yan rigarsa maimakon sunansa na ƙarshe don guje wa kamanceceniya da ɗan’uwansa.

Jobe ya ce ɗan uwansa ya ji daɗi sosai a lokacinda ya koma Dortmund inda ya kira abin a matsayin Abin Alfahari lokacin da ya gano cewa ya tafi Dortmund, ɗan wasan tsakiyar, wanda yawanci ke dannawa gaba fiye da ɗan’uwansa, ya ce ba ya son zama babban tauraro a shafukan sada zumunta “Ba na so in zama abin tattaunawa a ƙafafen sada zumunta, na fiso in zama Ɗaya daga cikin ‘‘yan wasan da suka fi hazaƙa a kowane wasa.”

Labarai Masu Nasaba

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

Dortmund za ta buɗe kakar wasanta da Essen a zagayen farko na gasar cin kofin Jamus ranar 18 ga watan Agusta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JudeMadrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Next Post

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Related

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig
Wasanni

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

53 minutes ago
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

6 hours ago
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari
Wasanni

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

23 hours ago
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 
Wasanni

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

2 days ago
Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool
Wasanni

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

2 days ago
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida
Wasanni

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

4 days ago
Next Post
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.