• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Ne Za A Dosa Wajen Daidaita Matsalar Sauyin Yanayin Duniya?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sauyin yanayi

Saura wata daya ke nan za a kawo karshen wannan shekarar da ya yiwu ta kasance mafi zafi a tarihin dan Adam, kuma a daidai wannan lokaci, aka kaddamar da taron bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo na 28(COP28) a birnin Dubai na hadaddiyar daular Larabawa.

Sai dai kuma a yankin Kahon Afrika, kasashen Kenya da Habasha da Somaliya na fuskantar ambaliyar da yanayin da ake kira Elnino ke haifarwa, biyo bayan mummunan bala’in fari da ba a taba ganin irinsa ba cikin shekaru 40 da suka wuce, da ya afka musu ba da jimawa ba.

  • Labarin Zamanintarwa Irin Na Kasar Sin: Kimiyya Na Taimakawa Manoma Fita Daga Kangin Talauci
  • Ya Kamata The British Museum Ta Mayar Da Kayayyakin Al’adu Da Aka Sace

Nazarin da aka gudanar ya shaida cewa, irin munanan yanayin da aka fuskanta a yankin kahon Afirka na da alaka da matsalar sauyin yanayi da ayyukan dan Adam suka haifar. Don haka ma, shugaban kasar Kenya William Ruto a yayin ziyarar da ya kai Turai a kwanan baya, ya yi gargadin cewa, Afirka na kara fuskantar matsalar yanayi.

Abin haka yake, sabo da abin da ya faru a yankin kahon Afirka yana kuma faruwa a sauran sassan nahiyar Afirka. Idan ba a manta ba, a bara, ambaliya da ta afkawa Nijeriya ta kasance mafi muni ga kasar cikin shekaru 10 da suka wuce, wadda ta halaka sama da mutane 600, tare da raba wasu miliyan 1.3 da muhallansu, baya ga yadda ta lalata gidaje kimanin dubu 82 da ma gonaki masu fadin eka dubu 110.

To, a irin wannan halin da ake ciki na kara samun zafin yanayi da ma bala’u daga indallahi, kasa da kasa ma na kara fahimtar muhimmancin daukar matakai na tinkarar sauyin yanayi. Taron COP28 da ke gudana a Dubai ya samu halartar mutane sama da dubu 70, abin da ya sa ya kasance mafi kasaita a tarihin taron, wanda ya shaida yadda kasa da kasa suke dora muhimmanci a kan batun tinkarar sauyin yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Kasar da ke karbar bakuncin taron ta kasance kasa ta biyar a duniya wajen yawan samar da man fetur, duk da haka, kasar na ganin dole ne a sauya fasalin makamashin da ake amfani da su.A yankin hamadar da ke kusa da birnin Abu Dhabi, babban birnin kasar, akwai wata tashar samar da wuta da makamashin rana da ta kasance irinta mafi girma a duniya, wadda wani kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin gina ta, tashar da ake kira Al Dhafra. An ce, tashar na iya biyan bukatun magidanta kimanin dubu 200, wadda kuma za ta rage iskar Carbon da ake fitarwa da kimanin ton miliyan 2.4, kwatankwacin yawan iskar Carbon da motoci dubu 500 ke fitarwa.

Sai dai ba wani abin mamaki ba ne yadda kamfanin kasar Sin ya samar da wannan tasha da ta kasance irinta mafi girma a duniya, sakamakon yadda kullum kasar Sin ke dora matukar muhimmanci a kan kiyaye muhalli, wadda take daukar kwararan matakai na tinkarar matsalar sauyin yanayi.

A nan kasar, akwai tsarin samar da makamashi mai tsabta mafi girma a duniya, kuma kasar ta kasance kasar da iskarta ta fi saurin inganta da ma kasar da dazuzzukanta suka fi saurin karuwa cikin shekaru 20 da suka wuce.

A sa’i daya kuma, kasar Sin ta yi kokarin sa kaimi ga aikin daidaita matsalar sauyin yanayin duniya, wadda ta aiwatar da ayyukan irinsu tashar Al Dhafra a sassan duniya. Misali, a Afirka, tashar samar da wuta da makamashin rana ta Garissa, wadda kamfanin kasar Sin ne ya gina, ta kasance mafi girma a gabashin Afirka,kuma bayan da aka fara aiki da ita a shekarar 2019, tana samar da wuta sama da KW miliyan 76 a kowace shekara, wadda ke iya biyan bukatun mutane sama da dubu 380, wadda ta yi matukar saukaka matsalar karancin wutar lantarki da aka fuskanta a wurin.

Yanzu haka wakilan kasa da kasa na haduwa a wajen taron COP28 a Dubai, don gano bakin zaren warware matsalar sauyin yanayi da ke addabar dan Adam. Kasar Sin a nata bangaren, na fatan hada kai da bangarori daban daban, don samar da karin gudummawa da dabaru wajen daidaita matsalar sauyin yanayin duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka
Daga Birnin Sin

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Next Post
Shi Mai Kula Da Babban Aiki Ne 

Shi Mai Kula Da Babban Aiki Ne 

LABARAI MASU NASABA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.