ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Ne Za A Dosa Wajen Daidaita Matsalar Sauyin Yanayin Duniya?

by CGTN Hausa
3 years ago
Sauyin yanayi

Saura wata daya ke nan za a kawo karshen wannan shekarar da ya yiwu ta kasance mafi zafi a tarihin dan Adam, kuma a daidai wannan lokaci, aka kaddamar da taron bangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo na 28(COP28) a birnin Dubai na hadaddiyar daular Larabawa.

Sai dai kuma a yankin Kahon Afrika, kasashen Kenya da Habasha da Somaliya na fuskantar ambaliyar da yanayin da ake kira Elnino ke haifarwa, biyo bayan mummunan bala’in fari da ba a taba ganin irinsa ba cikin shekaru 40 da suka wuce, da ya afka musu ba da jimawa ba.

  • Labarin Zamanintarwa Irin Na Kasar Sin: Kimiyya Na Taimakawa Manoma Fita Daga Kangin Talauci
  • Ya Kamata The British Museum Ta Mayar Da Kayayyakin Al’adu Da Aka Sace

Nazarin da aka gudanar ya shaida cewa, irin munanan yanayin da aka fuskanta a yankin kahon Afirka na da alaka da matsalar sauyin yanayi da ayyukan dan Adam suka haifar. Don haka ma, shugaban kasar Kenya William Ruto a yayin ziyarar da ya kai Turai a kwanan baya, ya yi gargadin cewa, Afirka na kara fuskantar matsalar yanayi.

ADVERTISEMENT

Abin haka yake, sabo da abin da ya faru a yankin kahon Afirka yana kuma faruwa a sauran sassan nahiyar Afirka. Idan ba a manta ba, a bara, ambaliya da ta afkawa Nijeriya ta kasance mafi muni ga kasar cikin shekaru 10 da suka wuce, wadda ta halaka sama da mutane 600, tare da raba wasu miliyan 1.3 da muhallansu, baya ga yadda ta lalata gidaje kimanin dubu 82 da ma gonaki masu fadin eka dubu 110.

To, a irin wannan halin da ake ciki na kara samun zafin yanayi da ma bala’u daga indallahi, kasa da kasa ma na kara fahimtar muhimmancin daukar matakai na tinkarar sauyin yanayi. Taron COP28 da ke gudana a Dubai ya samu halartar mutane sama da dubu 70, abin da ya sa ya kasance mafi kasaita a tarihin taron, wanda ya shaida yadda kasa da kasa suke dora muhimmanci a kan batun tinkarar sauyin yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Kasar da ke karbar bakuncin taron ta kasance kasa ta biyar a duniya wajen yawan samar da man fetur, duk da haka, kasar na ganin dole ne a sauya fasalin makamashin da ake amfani da su.A yankin hamadar da ke kusa da birnin Abu Dhabi, babban birnin kasar, akwai wata tashar samar da wuta da makamashin rana da ta kasance irinta mafi girma a duniya, wadda wani kamfanin kasar Sin ya dauki nauyin gina ta, tashar da ake kira Al Dhafra. An ce, tashar na iya biyan bukatun magidanta kimanin dubu 200, wadda kuma za ta rage iskar Carbon da ake fitarwa da kimanin ton miliyan 2.4, kwatankwacin yawan iskar Carbon da motoci dubu 500 ke fitarwa.

Sai dai ba wani abin mamaki ba ne yadda kamfanin kasar Sin ya samar da wannan tasha da ta kasance irinta mafi girma a duniya, sakamakon yadda kullum kasar Sin ke dora matukar muhimmanci a kan kiyaye muhalli, wadda take daukar kwararan matakai na tinkarar matsalar sauyin yanayi.

A nan kasar, akwai tsarin samar da makamashi mai tsabta mafi girma a duniya, kuma kasar ta kasance kasar da iskarta ta fi saurin inganta da ma kasar da dazuzzukanta suka fi saurin karuwa cikin shekaru 20 da suka wuce.

A sa’i daya kuma, kasar Sin ta yi kokarin sa kaimi ga aikin daidaita matsalar sauyin yanayin duniya, wadda ta aiwatar da ayyukan irinsu tashar Al Dhafra a sassan duniya. Misali, a Afirka, tashar samar da wuta da makamashin rana ta Garissa, wadda kamfanin kasar Sin ne ya gina, ta kasance mafi girma a gabashin Afirka,kuma bayan da aka fara aiki da ita a shekarar 2019, tana samar da wuta sama da KW miliyan 76 a kowace shekara, wadda ke iya biyan bukatun mutane sama da dubu 380, wadda ta yi matukar saukaka matsalar karancin wutar lantarki da aka fuskanta a wurin.

Yanzu haka wakilan kasa da kasa na haduwa a wajen taron COP28 a Dubai, don gano bakin zaren warware matsalar sauyin yanayi da ke addabar dan Adam. Kasar Sin a nata bangaren, na fatan hada kai da bangarori daban daban, don samar da karin gudummawa da dabaru wajen daidaita matsalar sauyin yanayin duniya.

Sauyin yanayi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

MASU ALAKA

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Next Post
Shi Mai Kula Da Babban Aiki Ne 

Shi Mai Kula Da Babban Aiki Ne 

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.