• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina So A Rika Tunawa Da Ni A Kan Kyawawan Halaye Da Cika Alkawari – Fatima Abdullahi

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adon Gari
0
Ina So A Rika Tunawa Da Ni A Kan Kyawawan Halaye Da Cika Alkawari – Fatima Abdullahi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

FATIMA ABDULLAHI matashiyar ‘yar kasuwa mai kokarin nema na nn kanta, a cikin tattunawarsu da BILKISU TIJJANI ALKASSIM, ta bayyana irin nasarorin da ta samu a harkar kasuwancinta, gami da kira ga mata da su tashi tsaye wajen neman na kansu domin neman rufin asiri. Har ila yau, ta tabo wasu batutuwa da suka shafi rayuwa. Ga dai yadda hirar tasu ta kasance:

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Fatima Abdullahi Muhammad, iyaye na haifaffun ‘yan jihar jigawa ne a cikin Karamar hukumar Hadejia. Na girma a garin Kano na yi makaranta a Kano kuma ni ce ta farko a wajen mamana da babana. Wannan ne takaitaccen tarihina.

Shin Fatima matar aure ce, ko dai ana niyya?

 A’a ni bani da aure, mun dai yi niyya in sha Allah

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

An kusa auran kena?

Eh to kin san da ke aure mukaddari ne daga ubangiji sai ki ga wani idan ya zo babu bata lokaci an yi shi duk zaman da ka yi sai ki ga ya wuce an manta da shi. Yanzu dai gaskiya takamaimai babu maganar aure muna sa ran Allah ya kawo mana miji nagari.

‘Yar kasuwa ce ko kuma ma’aikaciya?

Eh ni ‘yar kasuwa ce, ina saida abubuwa

Kamar wadanne irin abubuwa kie sayarwa?

Ina sai da abubuwa da dama

Shin me kasuwancin naki ya kunsa ma’ana kamar me da me kike sarrafawa?

Ina saida atamfofi, lashina, Da kuma kayan kicin, duk wani abu da kika sani na amfanin mata a kicin ina saidawa kowane iri in sha Allahu za ki samu a wajena.

Me ya ja hankalinki har kika shiga wannan kasuwanci?

Eh to a gaskiya ni tun ina karama ina ganin ana kasuwanci kuma tun lokacin yake matukar burge ni har na kirma ina sha’awar kasuwanci kuma yana matukar birge ni, ni dai ina sha’awar na zama mai saye da sayarwa.

Yaya matakin karatunki?

Matakin karatuna shi ne N.C.E. daga nan na tsaya ban ci gaba ba.

Yanzu kina sha’awar ci gaba ne ko kuma kasuwancin kika sa a gaba?

Gaskiya ina da ra’ayin ci gaba da karatu kuma in sha Allahu ina sa ran hakan.

Wane irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

A gaskiya kin san ko wace sana’a ba ta rasa kalubale sai dai mu ce Alhamdu lillah. Babban kalubalena shi ne bai wuci maganar bashi ba, mutane su dauki kaya ba sa son biyan kudi, wani idan kai masa magana ya nemi ya gaya maka maganar banza kai da kayanka, wani kuma ma ba zai bayar ba sai ka zo ka yi ta rigima har ka barshi, wasu kuma ba sa san daukan kayan idan ba su da kudi wadanda ke tsoron Allah kenan, wani kuma idan ya dauka daga ya samu zai bayar. To kin gani ba za’a taba kasuwanci a ce babu bashi ba sai dai ka san wanda za ka ba wa. Allah ya bamu kasuwa mai albarka.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika cimma?

Alhamdu lillah mun samu nasarori da dama ana ta samun ci gaba, kasuwanci yana ta bunkasa sosai ma. Allah mun gode maka.

Wane abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Ina matukar jin dadi wajen biya ma kaina bukatu ba tare da na tambaya a yi min ba wannan gaskiya yana faranta min rai sosai har ma ina taimaka wa wasu Alhamdu lillah.

Ta wacce hanya kike bi wajen tallata sana’arki?

Kafar sada dumunta, kamar WhatsApp, Facebook, instagram, da dai sauransu.

Dame kike so mutane su rinka tunawa da ke?

Kyawawan halaye da kuma kokarin cika alkawarina, sannan idan mutum ya sayi kayana hankalina baya kwanciya har sai kayan ya shiga hannunsa ya tabbatar min da abin da ya saya ya samu.

Ga sana’a, ga kuma hidimomin yau da kullum, shin ta yaya kike samun damar gudanar da hutunki?

Sana’a ta na saka a gaba gaskiya, sannan kuma sana’ata ba ta hanani yin wani abu, ba ta kuma hanani hutawa.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

A ce min Allah ya jikan mahaifiyata a gaskiya duk wanda ya ce min Allah ya jikan mahaifiyata ba karamin jin dadi nake ba kuma wanda ya fada min yana shiga raina.

Wane irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Sun bani goyan baya dari bisa dari.

Kawaye fa?

Suma suna bani hadin kai sosai suna kuma taya ni tallata kayana ina gode musu.

Me kika fiso cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Cikin kayan sawa na fi son abaya ko atamfa, kayan kwalliya kuma gaskiya ni abociyar kwalliya ce ina son kowanne in dai zan yi amfani da shi ya yi min kyau to gaskiya ina son sa.

A karshe wace irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Su dage da neman na kansu, kum su rike mutuncinsu a duk inda suke. Sannan kuma su rike gaskiya da amana a kowane hali mutum ya tsinci kansa Allah zai kawo mafita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cafke Wani Mutum Bisa Zargin Lalata Da ‘Yar Shekara 15

Next Post

Halin Da Wasu Jam’iyyun Siyasa Suka Tsinci Kansu

Related

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

2 weeks ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

3 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

4 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

5 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

5 months ago
Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
Adon Gari

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

6 months ago
Next Post
Halin Da Wasu Jam’iyyun Siyasa Suka Tsinci Kansu

Halin Da Wasu Jam'iyyun Siyasa Suka Tsinci Kansu

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.