• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Za Ta Biya Ma’aikata Sama Da 16,000 Alawus Daga Kasafin Naira Biliyan 18 Da Aka Ware Mata – Yakubu

by Sulaiman
2 years ago
Inec

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa, hukumar ta nemi naira biliyan 18 daga kasafin naira tiriliyan 2.17 ne domin ta biya ma’aikatanta sama da 16,000 kuɗaɗen alawus ɗin da gwamnatin tarayya ta yi musu ƙari acikin 2023.

Yakubu ya ce, jama’a sun yi wa hukumar yarfen cewa ta kashe makudan kudi har naira biliyan 335 na kasafin 2022 a zaɓen 2023.

  • Dalilan Da Suka Sanya Dole Nijeriya Ta Rungumi Fasaha Domin Bunkasa Tattalin Arziki
  • Matar Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar Da Bada Tallafin N50,000 Ga Mata Dubu 4 A Gusau

Don haka, hukumar ta ce, naira biliyan 18 da aka ware mata a wannan kasafin ƙarshen 2023, ba a zaɓuɓɓukan gwamnonin Bayelsa, Kogi da Imo za ta kashe su ba kadai.

Da ya ke jawabi a gaban Kwamitin Majalisar Tarayya a ranar Laraba, Yakubu ya ce, mafi yawancin kuɗaɗen duk wajen biyan ma’aikata za su tafi.

Yakubu ya ce, hukumar INEC na buƙatar naira biliyan 10.6 domin biyan ma’aikatanta ƙarin kashi 40 ciki 100 na alawus ɗin da Gwamnatin Tarayya ta yi musu. INEC na da ma’aikata 16,624.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Ya ce: “Za ku iya tunawa acikin watan Afrilu na wannan shekarar, an yi wa mai’aikatan gwamnatin tarayya ƙarin wasu kuɗaɗen alawus har zuwa kashe 40 cikin 100. To mu babu wannan ƙarin a cikin kasafin INEC na 2023, saboda an riga an rattabawa kasafin 2023 hannu a majalisa tun cikin Disamba, 2022. A watan Fabrairu gwamnatin tarayya ta fitar da sanarwar cewa an ƙara wa ma’aikatan gwamnati kashi 40 cikin 100 na alawus ɗin DTA da wasu alawus daban.

“INEC tana da ma’aikata sama da 15,000. Kuma a yanzu babu yadda za a iya samun kuɗaɗen da za a biya su, idan ba a bijiro da ƙwarya-ƙwaryan kasafin a ƙarshen wannan shekara ba.

“Dalili kenan muka gabatar da buƙatun kuɗaɗen ga gwamnati, don haka aka saka INEC cikin wannan kasafi.

Yakubu ya ci gaba da bayyana yadda hukumar zaɓe ta kashe naira biliyan 355 na cikin kasafin 2022, inda ya ce, akwai sauran kudaden a tare da hukumar.

Hukumar ta yi amfani da wani kaso na kuɗin wajen shirya zaɓen jihar Osun da Ekiti, yanzu kuma tana shirin gudanar da zaɓen Bayelsa, Imo duk da sauran kuɗaɗen.

Ya ce a yanzu sun nemi Naira biliyan 18 ne daga gwamnati saboda biyan ma’aikata alawus ɗin su da kuma biyan wasu sauye-sauye da aka samu na daga tashin farashin wasu kayayyaki a yanzu, kamar litar fetur, wadda aka kasafta ta akan naira 197 duk lita amma yanzu kuma ta haura Naira N600.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

Abin Da Ya Kamata A Sani Kan Noman Alkama Na Rani

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.