• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Za Ta Biya Ma’aikata Sama Da 16,000 Alawus Daga Kasafin Naira Biliyan 18 Da Aka Ware Mata – Yakubu

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Zaɓen Gwamna A Jihohi 3: INEC Ta Wallafa Cikakken Bayanan Katittikan Masu Zaɓe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa, hukumar ta nemi naira biliyan 18 daga kasafin naira tiriliyan 2.17 ne domin ta biya ma’aikatanta sama da 16,000 kuɗaɗen alawus ɗin da gwamnatin tarayya ta yi musu ƙari acikin 2023.

Yakubu ya ce, jama’a sun yi wa hukumar yarfen cewa ta kashe makudan kudi har naira biliyan 335 na kasafin 2022 a zaɓen 2023.

  • Dalilan Da Suka Sanya Dole Nijeriya Ta Rungumi Fasaha Domin Bunkasa Tattalin Arziki
  • Matar Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar Da Bada Tallafin N50,000 Ga Mata Dubu 4 A Gusau

Don haka, hukumar ta ce, naira biliyan 18 da aka ware mata a wannan kasafin ƙarshen 2023, ba a zaɓuɓɓukan gwamnonin Bayelsa, Kogi da Imo za ta kashe su ba kadai.

Da ya ke jawabi a gaban Kwamitin Majalisar Tarayya a ranar Laraba, Yakubu ya ce, mafi yawancin kuɗaɗen duk wajen biyan ma’aikata za su tafi.

Yakubu ya ce, hukumar INEC na buƙatar naira biliyan 10.6 domin biyan ma’aikatanta ƙarin kashi 40 ciki 100 na alawus ɗin da Gwamnatin Tarayya ta yi musu. INEC na da ma’aikata 16,624.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Ya ce: “Za ku iya tunawa acikin watan Afrilu na wannan shekarar, an yi wa mai’aikatan gwamnatin tarayya ƙarin wasu kuɗaɗen alawus har zuwa kashe 40 cikin 100. To mu babu wannan ƙarin a cikin kasafin INEC na 2023, saboda an riga an rattabawa kasafin 2023 hannu a majalisa tun cikin Disamba, 2022. A watan Fabrairu gwamnatin tarayya ta fitar da sanarwar cewa an ƙara wa ma’aikatan gwamnati kashi 40 cikin 100 na alawus ɗin DTA da wasu alawus daban.

“INEC tana da ma’aikata sama da 15,000. Kuma a yanzu babu yadda za a iya samun kuɗaɗen da za a biya su, idan ba a bijiro da ƙwarya-ƙwaryan kasafin a ƙarshen wannan shekara ba.

“Dalili kenan muka gabatar da buƙatun kuɗaɗen ga gwamnati, don haka aka saka INEC cikin wannan kasafi.

Yakubu ya ci gaba da bayyana yadda hukumar zaɓe ta kashe naira biliyan 355 na cikin kasafin 2022, inda ya ce, akwai sauran kudaden a tare da hukumar.

Hukumar ta yi amfani da wani kaso na kuɗin wajen shirya zaɓen jihar Osun da Ekiti, yanzu kuma tana shirin gudanar da zaɓen Bayelsa, Imo duk da sauran kuɗaɗen.

Ya ce a yanzu sun nemi Naira biliyan 18 ne daga gwamnati saboda biyan ma’aikata alawus ɗin su da kuma biyan wasu sauye-sauye da aka samu na daga tashin farashin wasu kayayyaki a yanzu, kamar litar fetur, wadda aka kasafta ta akan naira 197 duk lita amma yanzu kuma ta haura Naira N600.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKasafin 2023Majalisar Dattawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Barazanar Da Noman Masara Da Wake Ke Fuskanta A Nahiyar Afirka

Next Post

Abin Da Ya Kamata A Sani Kan Noman Alkama Na Rani

Related

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

56 minutes ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

2 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

16 hours ago
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
Labarai

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

18 hours ago
Next Post
Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

Abin Da Ya Kamata A Sani Kan Noman Alkama Na Rani

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.