ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Kamata A Sani Kan Noman Alkama Na Rani

by Abubakar Abba
3 years ago
Rani

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Nan da ‘yan kwanaki kadan za a fara yin noman rani na alkama, musamman a Jihohin Kano, Katsina, Kaduna, Bauchi, Taraba, Kebbi, Jigawa, Sokoto, Gombe da sauransu.

Tsohon Kwamishinan Ma’aikatar Aikin Noma na Jihar Gombe, kuma guda cikin manyan manoma, Alhaji Muhammad Magaji Gettado ya bayyana cewa, manoman da suka yi shuka bayan ranar 15 ga watan Nuwamba, za su iya samun matsala ko tangarda a gonakinsu.

  • Kungiyoyi Sun Nemi Majalisar Dattawa Ta Sa Baki A Cire Karamin Ministan Tsaro
  • GORON JUMA’A

 Sannan ya kuma yi kira ga Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, da ta tabbatar tana tallafa wa manoman alkama a kan lokaci, inda ya yi nuni da cewa, dabi’ar raba wa manona kayan aikin noma a makare ne ke jawo wa manoman kasar nan rashin samun amfani mai yawa bayan sun yi girbi.

Sai dai, wasu kwararru a fannin noman alkamar sun bai wa manoman kwarin guiwar cewa, za su iya yin shuka daga ranar 15 ga watan Nuwamba zuwa ranar 15 ga watan Disamba.

Kazalika, sun bayyana cewa; wadanda suke son su samu girbi mai yawa, za su iya yin shuka a makon farko na watan Nuwamba, ganin cewa alkama ta fi bukatar yanayin sanyi.

Daya daga cikin kwararru a wannan fanni kuma shugaban kungiyar masu sarrafa wa da kasuwancin alkama na kasa, Kwamanda Sojin Sama, mai ritaya Shuaibu Hamza ya sanar da cewa, kungiyar ta ware akalla kadada 77,000 domin yin noman alkama na rani.

Ya kara da cewa, a Jihar Neja akalla akwai kadadar yin noma kimanin 40,000, inda ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu manoman nata su kimanin 20,000 ne suka yi rijista, domin fara yin noman wannan alkama na rani.

Bugu da kari, a mako biyu da suka gabata ne, Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Raya Karkara da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya za ta noma kimanin kadada 70,000 a jihohin kasar nan da ke yin noman alkama, wadda ake sa ran za a samu girbin da ya kai na tan 875,000 domin adanawa.

Abubakar ya kara cewa, za a ware kadada 40,000 a Jihar Jigawa, sauran kadada 30,000 kuma za a raba su ga sauran jihohin da ke noman alkamar.

Wannan yana nuna cewa, Jihar Jigawa ita ce ta fi samun kaso mafi yawa, sakamakon jajircewar da take da shi a wannan fanni na noman alkamar, inda ta yi kokarin ware har kimanin kadada 40,000.

Rani
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

Ba Da Yawun Bakinmu Rarara Ya Yi Magana Ba -Ƙungiyar Mawaƙan Hausa

LABARAI MASU NASABA

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

September 12, 2026
An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

September 12, 2026
Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

September 12, 2026
Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Sanata Yari Ya Gudanar Da Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

September 12, 2026
Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

September 12, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Jam’iyyar APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Gwamnoni A Nijeriya -Dikko Raɗɗa

September 12, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.