• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Za Ta Gudanar Da Zaɓuɓɓuka 34 Cikin Fabrairun 2024 – Yakubu

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC), ta bayyana cewa mai yiwuwa a satin farko na watan Fabrairu, 2024 za ta gudanar da ragowar zaɓuɓɓukan da za a sake da kuma na cike gurabu a wasu mazaɓu, yankuna da shiyyoyin tarayya da jihohi.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a taron da INEC ta yi da jam’iyyun siyasa a ranar Litinin, a Abuja.

  • Manyan Hafsoshin Sojan Nijeriya Sama Da 113 Sun Yi Ritaya Daga Aikin Soja
  • Wani Mutum Ya Halaka Sakataren Kotu Har Lahira A Jihar Adamawa

Yakubu ya ce, INEC ta ɗaura aniyar gudanar da zaɓuɓɓukan biyu – zaɓukan da za a sake da kuma waɗanda ba a samu gudanarwa ba duk a rana ɗaya.

“Abin da ya rage shi ne hukumar zaɓe ta gudanar da zaɓuɓɓukan da kotuna suka bada umarnin a sake a wuraren da za a sake zaɓuɓɓukan.

“Kamar yadda ku ka sani, shi zaɓe na ‘re-run’, zaɓe ne da ya ƙunshi jam’iyyu da ‘yan takara waɗanda suka rigaya suka fafata a babban zaɓe. Sai fa idan jam’iyya na buƙatar musanya ɗan takara idan ya rasu kafin a sake wannan zaɓen da za a yi.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

“Shi kuma ‘bye-election’, zaɓe ne sabo da za a yi. Don haka, a wannan tsari, tilas ne jam’iyyu su sake gudanar da zaɓen fidda gwanaye cikin ƙa’idar kwanakin da dokar zaɓe ta gindaya.

“Zuwa yanzu dai Kotunan Ɗaukaka Ƙararrakin Zaɓe sun umarci INEC ta gudanar da zaɓuɓɓuka a mazaɓu 34 da suka ƙunshi shiyyar sanata ɗaya, sai mazaɓun ɗan majalisar tarayya guda 11 da majalisun jihohi 22.

“Sai dai kuma daga zaɓuɓɓuka 34 ɗin da za a sake, wurare uku ne kawai za a sake zaɓen baki ɗaya.”

A ƙarshe Yakubu ya ce sai bayan an kammala sauraren shari’un zaɓen gwamnoni a Kotun Ƙoli, sannan INEC za ta tattara yawan shari’un da aka gudanar, domin yin bayanin su dalla-dalla.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKotun KoliShari'ar Gwamnan Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Akpabio Ya Rantsar Da Lalong A Matsayin Sanata Mai Wakiltar Filato Ta Kudu

Next Post

Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

4 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

6 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

7 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

8 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

11 hours ago
Next Post
Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba

Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.