• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Za Ta Gudanar Da Zaɓuɓɓuka 34 Cikin Fabrairun 2024 – Yakubu

by Sulaiman
2 years ago
kogi

Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC), ta bayyana cewa mai yiwuwa a satin farko na watan Fabrairu, 2024 za ta gudanar da ragowar zaɓuɓɓukan da za a sake da kuma na cike gurabu a wasu mazaɓu, yankuna da shiyyoyin tarayya da jihohi.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a taron da INEC ta yi da jam’iyyun siyasa a ranar Litinin, a Abuja.

  • Manyan Hafsoshin Sojan Nijeriya Sama Da 113 Sun Yi Ritaya Daga Aikin Soja
  • Wani Mutum Ya Halaka Sakataren Kotu Har Lahira A Jihar Adamawa

Yakubu ya ce, INEC ta ɗaura aniyar gudanar da zaɓuɓɓukan biyu – zaɓukan da za a sake da kuma waɗanda ba a samu gudanarwa ba duk a rana ɗaya.

“Abin da ya rage shi ne hukumar zaɓe ta gudanar da zaɓuɓɓukan da kotuna suka bada umarnin a sake a wuraren da za a sake zaɓuɓɓukan.

“Kamar yadda ku ka sani, shi zaɓe na ‘re-run’, zaɓe ne da ya ƙunshi jam’iyyu da ‘yan takara waɗanda suka rigaya suka fafata a babban zaɓe. Sai fa idan jam’iyya na buƙatar musanya ɗan takara idan ya rasu kafin a sake wannan zaɓen da za a yi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

“Shi kuma ‘bye-election’, zaɓe ne sabo da za a yi. Don haka, a wannan tsari, tilas ne jam’iyyu su sake gudanar da zaɓen fidda gwanaye cikin ƙa’idar kwanakin da dokar zaɓe ta gindaya.

“Zuwa yanzu dai Kotunan Ɗaukaka Ƙararrakin Zaɓe sun umarci INEC ta gudanar da zaɓuɓɓuka a mazaɓu 34 da suka ƙunshi shiyyar sanata ɗaya, sai mazaɓun ɗan majalisar tarayya guda 11 da majalisun jihohi 22.

“Sai dai kuma daga zaɓuɓɓuka 34 ɗin da za a sake, wurare uku ne kawai za a sake zaɓen baki ɗaya.”

A ƙarshe Yakubu ya ce sai bayan an kammala sauraren shari’un zaɓen gwamnoni a Kotun Ƙoli, sannan INEC za ta tattara yawan shari’un da aka gudanar, domin yin bayanin su dalla-dalla.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba

Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.