• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ingila Ta Rage Haraji Kan Kayayyakin Nijeriya 3,000

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Ingila

Kasar Ingila ta sanar da matakin da ta dauka na rage haraji kan kayayyakin da ake shigar mata daga kasar Nijeriya sama 3,000, a karkashin wani shiri bunkasa kasuwancin kasashe masu tasowa (DCTC).

Jakadar kasar Ingila a Nijeriya, Richard Montgomery, shi ne ya shaida hakan a Abuja ranar Talata a wajen wani taron kara wa juna sani kan shirin Ingila na bunkasa harkokin kasuwancin kasashe masu tasowa da aka shirya da hadin guiwar ma’aikatar kula da harkokin kasuwanci, cinikayya da zuba jari ta Nijeriya da kuma hukumar bunkasa fitar da kayayyakin Nijeriya zuwa kasashen waje (NEPC).

  • Mafi Yawan Matan Arewa Ba Sa Samun Horo Da Kwarin Gwiwa – Zainab Ado Bayero

Jakadar wanda ya samun wakilcin mataimakiyarsa, Misis Gill Atkinson, ya ce sun dauki matakin ne domin kyautatawa da bunkasa harkokin kasuwanci a tsakanin kasar Ingila da kuma Nijeriya.

“Shiri bunkasa hada-hadar kasuwancin kasashe masu tasowa na amfanar da kasashe 46, daga cikinsu kasashe 31 duk suna Afrika, kuma kasar da za ta zama muhimmiya a wannan bangaren ita ce Nijeriya.

“Wannan sabon tsarin cinikayyar ya fara aiki ne daga ranar 19 ga watan Yuli, kuma shi ne tsari mafi inganci da ke saurin saukawawa da bunkasa hada-hadar kasuwanci ga kowace kasa a fadin duniya. Kasar Ingila ta himmatu wajen kyautata dangartakarta da Nijeriya mai dadadden tarihi kuma da yunkurin ganin kowani bangare a tsakaninsu ta amfana da wannan alakar.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

“Nijeriya ce za ta fi kowace kasa morar sabon tsarin bunkasa hada-hadar kasuwanci na CTS. Domin kuwa an rage haraji ga kayayyakin Nijeriya sama da 3000 da ke nuni da kaso 99 cikin dari na kayayyakin da Nijeriya ke fitarwa zuwa kasar Ingila,” in ji shi.

Tun da farko a jawabinta, babbar sakatariya a ma’aikatar cinikayya da zuba hannun jari a Nijeriya, Dakta Ebelyn Ngige, da ta samu wakilcin daraktan kasuwanci na ma’aikatar, Suleiman Audu, ta ce sabon tsarin zai yi matukar taimakawa wajen bunkasar kayayyakin da Nijeriya ke fitarwa zuwa kasar.
Ta jinjina wa kasar Ingila bisa daukan wannan matakin, ta na mai cewa hakan zai kara kyautata alaka tsakanin kasashen biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

katsina
Labarai

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Abduljabbar
Labarai

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Next Post
Sojojin Nijeriya Sun Yi Taro Kan Shafukan Sada Zumunta A Kebbi

Sojojin Nijeriya Sun Yi Taro Kan Shafukan Sada Zumunta A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.