• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iska Yana Yawo Da Mai Kayan Kara

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Iska
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne cewa, kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma gwamnatin Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin, ita ce halastacciyar gwamnati kadai dake wakiltar kasar Sin.

Haka kuma kasancewar kasar Sin daya tilo a duk duniya, ita ce babbar manufar da kasashen duniya suka amince da ita, kana tushen siyasa na raya hulda tsakanin Sin da duk kasashen da suka kulla ko ma suke son kulla alaka da kasar Sin.

  • Manzon Musammam Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Zimbabwe

Kuma a maganar da ake, akwai kasashe sama da 100 a fadin duniya, wadanda suka amince tare da goyon bayan manufar kasar Sin daya tak a duniya, kuma wannan ita ce yarjejeniya ta zahiri da kasashen duniya suka amince da ita.

Wasu rahotanni na cewa, wai mahukuntan Taiwan sun gabatar da jerin “bukatu hudu” game da shigar yankin cikin MDD tare da yin ikirarin cewa, za su gayyaci “abokan diflomasiyya” don mika wa babban sakataren MDD wasikar tare, da ke neman ya gyara kuskuren da MDD ta yi wa kuduri mai lamba 2758 na babban taron MDD.

Wannan tamkar mafarki ne ko wasa da hankalin da wasu daga kasashen yamma ke yiwa jagororin yankin na Taiwan.

Labarai Masu Nasaba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Kowa ya san cewa, Taiwan ba kasa ba ce, wani bangare ne na kasar Sin. Kuma duk wani abun da ’yan aware da masu goya musu suke yi na neman jirkita gaskiya da ma neman tayar da hargitsi ko neman ballewa, ko kadan ba zai taba canja gaskiyar lamarin ba, wato babban yanki da kuma yankin Taiwan duka suna karkashin ikon Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ne.

Don haka, yankin Taiwan ba shi da tushe, ko hujja ko iko na shiga Majalisar Dinkin Duniya ko wasu kungiyoyin kasa da kasa da ke bukatar kasa ta zama mai ’yanci kafin ta shiga.

Duk wanda ya san tarihi ya san cewa, bangarorin biyu na mashigin tekun Taiwan na kasar Sin daya ne. Kuma Taiwan wani yanki ne na kasar Sin. Ko da yake bangarorin biyu sun dade suna adawa da juna a siyasance, amma hakan bai sa an taba raba ikon mallakar kasa da cikakken yankin kasar Sin ba. Wannan shi ne ainihin yanayin batun Taiwan.

Hasashen ko mafarkin da hukumomin DPP suka yi na shigar Taiwan cikin tsarin MDD, a hakika wani yunkuri ne na haifar da ra’ayi na karya game da kasar Sin a matsayin “kasar Sin kasashe biyu” ko “kasar Sin daya kuma Taiwan daya” da kuma kalubalantar tsarin kasa da kasa.

Ya kamata masu barci ko mafarki kan wannan gurguwar shawara, su farka, su kuma fahimci cewa, kasar Sin daya ce tak a duniya kuma Taiwan wani bangaren na kasar Sin da ba za a taba raba shi ba. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jirgin Kasa Dake Zirga-zirga Cikin Gari Da Sin Ta Gina Ya Fara Aiki A Lagos Na Najeriya

Next Post

Olympic 2024:Tobi Amusan Da Nathaniel Ezekiel Za Su Wakilci Nijeriya

Related

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
Daga Birnin Sin

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

2 hours ago
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

2 hours ago
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

3 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

4 hours ago
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

5 hours ago
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

6 hours ago
Next Post
Olympic 2024:Tobi Amusan Da Nathaniel Ezekiel Za Su Wakilci Nijeriya

Olympic 2024:Tobi Amusan Da Nathaniel Ezekiel Za Su Wakilci Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.