ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iska Yana Yawo Da Mai Kayan Kara

by CMG Hausa
3 years ago
Iska

Sanin kowa ne cewa, kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma gwamnatin Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin, ita ce halastacciyar gwamnati kadai dake wakiltar kasar Sin.

Haka kuma kasancewar kasar Sin daya tilo a duk duniya, ita ce babbar manufar da kasashen duniya suka amince da ita, kana tushen siyasa na raya hulda tsakanin Sin da duk kasashen da suka kulla ko ma suke son kulla alaka da kasar Sin.

  • Manzon Musammam Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Zimbabwe

Kuma a maganar da ake, akwai kasashe sama da 100 a fadin duniya, wadanda suka amince tare da goyon bayan manufar kasar Sin daya tak a duniya, kuma wannan ita ce yarjejeniya ta zahiri da kasashen duniya suka amince da ita.

ADVERTISEMENT

Wasu rahotanni na cewa, wai mahukuntan Taiwan sun gabatar da jerin “bukatu hudu” game da shigar yankin cikin MDD tare da yin ikirarin cewa, za su gayyaci “abokan diflomasiyya” don mika wa babban sakataren MDD wasikar tare, da ke neman ya gyara kuskuren da MDD ta yi wa kuduri mai lamba 2758 na babban taron MDD.

Wannan tamkar mafarki ne ko wasa da hankalin da wasu daga kasashen yamma ke yiwa jagororin yankin na Taiwan.

LABARAI MASU NASABA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Kowa ya san cewa, Taiwan ba kasa ba ce, wani bangare ne na kasar Sin. Kuma duk wani abun da ’yan aware da masu goya musu suke yi na neman jirkita gaskiya da ma neman tayar da hargitsi ko neman ballewa, ko kadan ba zai taba canja gaskiyar lamarin ba, wato babban yanki da kuma yankin Taiwan duka suna karkashin ikon Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ne.

Don haka, yankin Taiwan ba shi da tushe, ko hujja ko iko na shiga Majalisar Dinkin Duniya ko wasu kungiyoyin kasa da kasa da ke bukatar kasa ta zama mai ’yanci kafin ta shiga.

Duk wanda ya san tarihi ya san cewa, bangarorin biyu na mashigin tekun Taiwan na kasar Sin daya ne. Kuma Taiwan wani yanki ne na kasar Sin. Ko da yake bangarorin biyu sun dade suna adawa da juna a siyasance, amma hakan bai sa an taba raba ikon mallakar kasa da cikakken yankin kasar Sin ba. Wannan shi ne ainihin yanayin batun Taiwan.

Hasashen ko mafarkin da hukumomin DPP suka yi na shigar Taiwan cikin tsarin MDD, a hakika wani yunkuri ne na haifar da ra’ayi na karya game da kasar Sin a matsayin “kasar Sin kasashe biyu” ko “kasar Sin daya kuma Taiwan daya” da kuma kalubalantar tsarin kasa da kasa.

Ya kamata masu barci ko mafarki kan wannan gurguwar shawara, su farka, su kuma fahimci cewa, kasar Sin daya ce tak a duniya kuma Taiwan wani bangaren na kasar Sin da ba za a taba raba shi ba. (Ibrahim Yaya)

Iska
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar
Daga Birnin Sin

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku
Daga Birnin Sin

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Next Post
Olympic 2024:Tobi Amusan Da Nathaniel Ezekiel Za Su Wakilci Nijeriya

Olympic 2024:Tobi Amusan Da Nathaniel Ezekiel Za Su Wakilci Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

June 18, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

June 18, 2026
Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.